Yunwa na kashe ’yan Najeriya, amma Tinubu ko a jikinsa – Atiku
Published: 1st, October 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya yaba wa ’yan Najeriya bisa abin da ya kira ‘hakurinsu, juriya da kwazo’ duk da tsananin matsin tattalin arziki da rashin tsaro da suke fama da shi.
A cikin sakonsa na murnar cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai da ya aike ga ’yan kasa, Atiku ya zargi gwamnatin jam’iyyar APC da watsi da al’umma, yana mai cewa sun bar ’yan Najeriya su fama da rayuwa mai cike da kalubale ba tare da kulawa ba.
Atiku ya ce “’yan Najeriya na fama da tsananin rashin tsaro, karancin abinci, rashin aikin yi da kuma yanayi mai cike da fargaba da rashin kyakkyawar makoma wanda ya kara muni sakamakon rashin tausayi da rashin kulawar gwamnatin APC.
“Abin takaici ne cewa a cikin kasa mai albarka da arziki, miliyoyin mutane sun koma ’yan gudun hijira da mabarata a cikin kasarsu. Kowace gwamnati mai kishin kasa tana daukar rayuwa da tsaron ’yan kasa da muhimmanci.
“Amma abin da muke fama da shi a yau shi ne gwamnatin da ta watsar da jama’arta. Yunwa na kashe ’yan Najeriya, ’yan bindiga na hallaka al’umma, amma Shugaba Bola Tinubu da ministocinsa suna kallon abubuwa suna faruwa ba tare da nuna damuwa ba.”
Sai dai Atiku ya bukaci ’yan kasa da kada su yanke kauna, yana mai tunatar da su cewa shekarar 2027 na tafe da damar sauya shugabanci mara nagarta da kuma dawo da rayuwa mai kyau.
“Kyawun dimokuradiyya yana cikin ikon kada kuri’a. Ko da kuwa jama’a na cikin kunci da zalunci a yau, za su samu damar kawar da wannan gwamnati mara iya aiki a zabe mai zuwa. Wannan iko ne da babu wata kungiya da za ta iya kwacewa daga hannun jama’a,” in ji shi.
A cewarsa, duk da cewa Najeriya ta cika shekara 65 da samun ’yancin kai, har yanzu tana tafiyar hawainiya sakamakon shekaru da dama na shugabanci mara nagarta da almubazzaranci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano
Wasu mahara sun yi wa wasu matan aure biyu kisan gilla a gidan mijinsu da keunguwar Tudun Yola a Ƙaramar Hukumar Gwale ta Jihar Kano.
Aminiya ta samu rahoton cewa maharan banka wa gidan wuta bayan da suka soka wa ɗaya daga cikin matan wuka har lahira, ɗayar kuma an tsinci gawarsa a cikin banɗaki.
Matan da aka yi wa wannan kisan gilla — Hauwa’u Yakubu da Zahra’u Aliyu — mata ne ga wani mai suna Alhaji Ashirin Shu’aibu Usaini.
Al’unnar unguwar Tudun Yola sun shiga tashin hankali da wannanan ɗanyen aiki.
HOTUNA: Yadda Babban Taronjam’iyyar PDP ke gudana Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a BornoƊan mai gidan, Anas Shu’aibu, ya yi zargin ana yi wa matan mahaifinsa wannan kisan gilla ne da tsakar rana lokacin da mai gidan da ’ya’yansa suka fita.
“Ba mu san abin da ke faruwa ba sai da daddare bayan mahaifinsmu ta kira cewa ina dawo gida, muna zuwa muka ga ɗaya yaqar a ƙone, ɗayar muka an kulle ta a banɗaki, ko da muka ɓalle ƙofar sai muka samu ita ma ta riga ta mutu.
“Da farko mun yi zargin gobara ce, amma sai muka lura cewa da alamar hari aka kai musu.”
Alhaji Shu’aibu, cikin kaɗuwa ya bayyana cewa “sun kashe Matana, sun ƙona gawar ɗayar. Ban san dalilin wannan rashin imani ba.”
Kakakin ’yan sandan Jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Koyawa ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewa rundunar ta ta fara gudanar da bincike a kai.