Abin da ya faru a zaman sulhun PENGASSAN da Matatar Ɗangote
Published: 30th, September 2025 GMT
A ranar Talatar nan ake sa ran ci gaba da tattaunawa tsakanin Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur (PENGASSAN) da Kamfanin Matatar Man na Ɗangote kan taƙaddamar da ke tsakaninsu.
Ana sa ran za a ci gaba da zaman sulhun, wanda Gwamnatin Tarayya ta kira domin sasanta ɓangarorin ne zuwa da yamma.
Hakan ta faru ne bayan an tashi taron a cikin tsakar daren ranar Litinin ba tare da an cimma wata matsaya ba.
Gwamnatin Tarayya ta kira zaman sulhun ne bayan ƙungiyar PENGASSAN ta zargi Kamfanin Ɗangote da kora da kuma sauyin aikin mambobinta kimanin mutum 800.
PENGASSAN ta yi barazanar yajin aiki muddin ba a dawo da ma’aikatan ba, a yayin da kamfanin ke cewa ga sallame su ne saboda suna masa zagon ƙasa.
Taron, ya samu halarcin shugaban PENGASSAN, Festus Osifo, da wakilan Kamfanin Ɗangote, da sakataren TUC, Nuhu Toro, da wasu jami’an gwamnati. Ministan Kwadago, Maigari Dingyadi, ne ya jagoranci zaman tare da Ministan Kuɗi, Wale Edun.
A yayin jawabinsa na buɗe taron, Minista Dingyaɗi ya ja hankalin ɓangarorin cewa, “Abin da ke faruwa a yau yana da matuƙar muhimmanci ga tattalin arziƙinmu da tsaron ƙasa. Mun samu labarin cewa PENGASSAN ta kira yajin aiki.”
Bayan awannin ana tattaunawa, wani wanda ya halarci zaman ya shaida wa wakilinmu cewa wakilan Kamfanin Ɗangote sun ƙi amincewa da dawo da ma’aikatan da aka kora, inda suka kira su “masu zagon ƙasa”, lamarin da ya fusata shugabannin ƙwadagon.
“An ba kowanne ɓangare damar gabatar da buƙatunsu, amma duk sun nace a kan matsayinsu. Babu wanda ya yarda ya sassauta,” a cewar majiyar.
NLC ta shiga lamarinA gefe guda kuma, Ƙungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC) ta tura saƙo ga ƙungiyoyinta, tana zargin Kamfanin Ɗangote da take-taken tauye haƙƙin ma’aikata da karya doka.
A wata wasika da Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya aika, ƙungiyar ta ce kamfanin na “ƙoƙarin karya ƙungiyoyi, bautar da ma’aikata da kuma wulaƙanta doka,” tare da yin iƙirarin cewa ya daɗe yana aiki “kamar wata gwamnati a cikin gwamnati.”
Wasikar ta umarci rassan ƙungiyar da su fara gaggawar shirya mambobi tare da shirin tunkarar rassan kamfanin a faɗin ƙasa kan abin da suka kira “tsaurin kai ga doka.”
Ƙungiyar ta bukaci su kafa kwamitocin wayar da kai cikin sa’o’i 72, tare da haɗin gwiwa da sakatariyar NLC.
“Wannan rashin ladabi na Ɗangote dole ne a tunkare shi da ƙarfi daga ɓangaren ƙwadago,” in ji wasikar.
“Da gumin ma’aikatan Nijeriya ne suka gina wannan kamfani; ba za mu bari ya zama ana zaluntar su ba. Tare muke tsaye, tare za mu yi nasara.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗangote tattaunawa Yajin aiki Kamfanin Ɗangote
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya buƙaci al’umma su ƙara kula da tsaro tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, yayin da ’yan bindiga suka fara kai hare-hare a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina.
Sarkin, ya yi wannan kira ne yayin ziyarar jaje da ya kai wa al’ummar Faruruwa da ke Ƙaramar Hukumar Shanono a Jihar Kano.
Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16 Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — MuftwangA baya-bayan nan ’yan bindiga sun kai hari yankunan, inda suka sace shanu tare da yin garkuwa da mutane.
Sarki Sanusi, ya ce yawan hare-haren da ake fuskanta a yankin ya nuna cewa ana buƙatar kula da goyon bayan sarakunan gargajiya, gwamnati da kuma ƙungiyoyin sa-kai.
“Tsawon watanni da suka gabata, hare-hare sun ƙaru a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina, inda ’yan bindiga ke zuwa su sace shanu, su kashe jama’a, su yi garkuwa da maza da mata,” in ji shi.
Ya ce ya kai ziyarar ne domin jajanta wa mazauna yankin da abin ya shafa, tare da tabbatar musu da goyon bayan gwamnati, da kuma ƙarfafa musu gwiwa su taka rawa wajen kare ƙauyukansu.
“Nauyinmu ne a matsayinmu na shugabanni mu zo mu ga mutanenmu, mu yi musu ta’aziyya, mu kuma tabbatar musu cewa gwamnati da jami’an tsaro suna yin iya bakin ƙoƙarinsu,” ya ce.
Sarkin ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta tura jami’an tsaro da kayan aiki don tsaron yankin.
“Gwamna ya sayi motocin aiki, ya samar da kayan aiki, kuma mutane na gani da idonsu yadda sojoji da ’yan sanda ke yawan sintiri a yankin.
“Muna kuma ƙarfafa musu gwiwa su yi amfani da ’yan sa-kai wajen kare ƙauyukansu,” a cewarsa.
Sarki Sanusi, ya kuma bukaci al’ummomin Katsina da ke maƙwabtaka da yankunan da su tabbatar cewa yarjejeniyar sulhu da suke yi da ’yan bindiga ba za ta zama silar kawowa Kano hari ba.
Ya yi addu’ar Allah Ya wanzae da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa, tare da alƙawarin ci gaba da aiki tare da gwamnatin jihar domin kare rayukan jama’a.
“Muna rokon Allah Ya dawo mana da zaman lafiya, kuma za mu ci gaba da yin iya bakin ƙoƙarinmu tare da gwamnati domin tabbatar da tsaro a wannan jiha,” in ji shi.