Netanyahu ya ba da haƙuri kan harin Isra’ila a Qatar
Published: 30th, September 2025 GMT
Fira Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ba wa Gwamnatin ƙasar Qatar haƙuri kan harin da ƙasarsa ta kai a birnin Doha, wanda ya yi ajalin wani jami’in tsaron Qatar.
Netanyahu ya bayar da haƙuri ne a yayin wata tattaunawa da shugaban Amurka, Donald Trump ya shirya tsakaninsu da Fira Ministan Qatar, Mohammed Al-Thani.
A saƙon da Netanyahu ya wallafa a X, ya ce, “Mai girma Fira Minista, ina sanar da kai cewa Isara’ila ta yi nadamar abin da ya faru na rasuwar wani ɗan ƙasarka a harin da muka kai,” da makami mai linzamina ranar 9 ga watan Satumba a birnin Doha.
Fadar White House ta Amurka da Ma’aikatar Harkokin Wajen ƙasar Qatar sun tabbatar da tattaunawar, wadda Shugaba Donald Trump ya jagoranta.
Sanarwar da Fadar White House ta fitar ta ce, Netanyahu, “Ya bayyana matuƙar nadama bisa yadda harin makami mai linzamin ya yi ajalin jami’an tsaron Qatar a bisa kuskure.
“Kazalika ya bayyana nadamarsa da cewa harin da Isra’ila ta kai kan jagororin ƙungiyar Hamas, ya keta hurumin ’yancin Qatar a matsayin ƙasa, yana mai jaddada cewa hakan ba zai sake faruwa ba.”
Idan ba a manta ba a baya Isra’ila ta kai harin ne a yayin ake tattaunawa tsakaninta da wakilan ƙungiyar Hamas a birnin Doha. Ta bayyana cewa ta kai harin ne a kan wasu jagororin ƙungiyar Hamas, tana mai nanata cewa za ta maimaita irinsa idan bukatar hakan ta taso.
Bayan harin ‘—wanda ƙasashen duniya, har da Najeriya suka la’anta—ne Qatar ta dakatar da tattaunawar ɓangarorin Hamas da Isra’ila, wanda ke da nufin ganin ƙungiyar ta sako Isra’ilawan da ta yi garkuwa da kuma tsagaita wuta a Zirin Gaza.
Kazalika ta yi gargaɗin cewa ba za ta lamunci mummunar ɗabi’ar ta Isra’ila da ke barazana ga tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya ba.
Qatar ta kasance babban mai shiga tsakani domin sasanta rikicin Gaza, wanda ya ƙi ci ya ƙi cinyewa, kuma ita ce mai masauki ga babban sansanin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.
Ta bayyana godiya kan abin da Trump ya yi “Don hana maimatuwar hari kan ƙawarta, ƙasar Qatar, da kuma haɗin gwiwarsu ta fuskar tsaro.”
A saƙon da Netanyahu ya wallafa a X, ya bayyana ce, “Mai girma Fira Minista, ina sanar da kai cewa Isara’ila ta yi nadamar abin da ya faru na rasuwar wani ɗan ƙasarka a harin da muka kai.
“Amma ina so ka fahimci cewa ƙungiyar Hamas ce hadafinmu ba ’yan ƙasar Qatar ba.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Netanyahu Qatar ƙungiyar Hamas Netanyahu ya ƙasar Qatar
এছাড়াও পড়ুন:
Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno
Mayaƙan ƙungiyar ISWAP sun kashe wani babban kwamandan rundunar sojin Najeriya bayan wani harin kwantan ɓauna da aka kai wa tawagarsa a hanyar Damboa–Biu da ke Jihar Borno.
Lamarin ya faru ne bayan da tawagar sojojin tare da dakarun haɗin gwiwa na Civilian Joint Task Force (CJTF) suka kai wani samame a yankin, inda suka gamu da harin ba-zata na ’yan ta’adda.
’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a Gombe Hauhawar farashi ya ƙara raguwa a Nijeriya — NBSKwamandan, wanda daga baya aka bayyana sunansa a matsayin Brigade Commander M. Uba, shi ne ya jagoranci rundunar da ta kai ɗauki ga wasu sojoji da suka yi ɓatan hanya kafin su faɗa tarkon mayaƙan ISWAP.
PRNigeria ta ruwaito cewa, kafin rasuwarsa, kwamandan ya aike da wani bidiyo ga manyansa yana bayyana irin nasarar da tawagarsa ta samu a wani farmaki da suka kai.
Sai dai bayan haka ne ISWAP ta bibiyi wurin da yake ta katse sadarwa, sannan ta kama shi.
Rahotanni sun ce mayaƙan sun kama shi ne da ransa, inda bayan sun yi masa tambayoyi, daga bisani kuma su kashe shi.
Da farko dai rundunar sojin Najeriya ta ce kwamandan yana cikin ƙoshin lafiya bisa hujjar bidiyon da ya aika yana tabbatar da irin nasarar da suke samu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin ƙasa, Laftanar Kanar Appolonia Anele, ta bayyana batun cafke kwamandan nata a matsayin “ƙazon kurege”, tana mai cewa duk da “harbe-harbe masu tsanani” da suka fuskanta daga mayaƙan yayin dawowarsu daga sintiri a gefen Sambisa, an yi nasarar tsira da kwamandan.
Sanarwar ta tabbatar da mutuwar sojoji biyu da jami’an sa-kai biyu a harin, amma ta ce kwamandan ba ya cikin waɗanda aka kama.
Sai dai daga bisani, wasu rahotanni na PRNigeria da jaridar PREMIUM TIMES sun tabbatar da cewa mayaƙan ISWAP sun kama kwamanda ne bayan ya yi ɓata hanya yayin guje wa harin farko.
ISWAP ta yi iƙirarin kashe kwamandanA wata sanarwa cikin harshen Larabci da ISWAP ta wallafa ranar Litinin a jaridarta mai suna Amaq, ta nuna hoton kwamandan a lokacin da ya ke hannunta, yana fama rauni har jini na zuba a kafarsa.
Ƙungiyar ta ce: “Mun kama kwamandan rundunar Najeriya bayan ya tsere daga harin Wajiroko, daga nan muka yi masa tambayoyi sannan muka kashe shi.”
Ƙungiyar ta kuma yi wa rundunar sojin Najeriya gugar zana, tana mai bayyana bayanan farko da ta fitar a matsayin “ƙarya tsagwaronta da ke tabbatar da gazawarta.”
Kawo yanzu dai Rundunar Sojin Najeriya ba ta fitar da sanarwa a hukumance ba, amma majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa ana gudanar da bincike kan yadda aka bar kwamandan cikin haɗari bayan tserewa daga harin farko.