An Nada Shugaban Hukumar Fasahar Sadarwa Da Inganta Tattalin Arziki Ta Jihar Jigawa
Published: 4th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da nadin Dr. Mohammed Hassan a matsayin Darakta Janar na farko na Hukumar Fasahar Sadarwa da inganta Tattalin Arzikin ta fasahar zamani ta Jihar Jigawa.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya fitar a Dutse.
Kafin nadin nasa, Dr. Muhammad Hassan shi ne shugaban hukumar Fasahar Sadarwa da Kimiyya ta Jigawa, wato Galaxy ITT.
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa sabo shugaban hukumar ya sami digirinsa na farko a fannin Lissafi daga Jami’ar Bayero, Kano, a shekarar 2008. Daga bisani, ya samu digiri na biyu a fannin Kimiyyar Kwamfuta daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Afirka (AUST), Abuja, a shekarar 2011, sannan ya ci gaba da karatu har ya samu digirin digirgir (Ph.D) a fannin Kimiyyar Kwamfuta da Injiniyanci daga Jami’ar Aizu da ke kasar Japan, a 2018.
Haka nan, Gwamnan ya amince da naɗin Baffajo Beita a matsayin sabon shugaban Galaxy ITT.
Kafin naɗinsa, Beita Babban Jami’in Bayanan Fasaha ne a Galaxy Backbone da ke Abuja. Yana da ƙwarewa mai zurfi a fannin fasahar sadarwa, musamman a tsarin gudanar da cibiyoyin sadarwa, tsaro na yanar gizo, da ƙirƙirar fasahar yanar gizo.
Beita ya kammala digirinsa na farko a fannin Kwamfuta daga Jami’ar Anglia Ruskin, kuma ya fara aikinsa ne a Makarantar Informatics ta Jihar Jigawa da ke Kazaure, kafin ya taka muhimmiyar rawa a manyan ayyukan fasahar sadarwa a Turai, Gabas ta Tsakiya, da Afirka (EMEA) a fannoni daban-daban, ciki har da masana’antar mai da gas, da sarrafa kayayyaki, da harkokin kuɗi”.
Bugu da ƙari, Gwamnan ya amince da naɗin Muhammad Nura Zubairu a matsayin Daraktan Zartarwa na Ayyukan Fasaha, da Umar Ibrahim Gumel a matsayin Daraktan Zartarwa na Harkokin Kasuwanci a Galaxy ITT.
Kafin wannan matsayi, Muhammad Nura ya kasance Injiniyan Tallafin Sadarwa a Galaxy ITT, kuma ya kammala babbar difloma (HND) a fannin Tattalin Arzikin Hadin Gwiwa da Gudanarwa daga Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010.
“Wadannan muhimman nade-nade na cikin shirye-shiryen Gwamna Namadi na ƙarfafa tattalin arzikin Jihar Jigawa ta fasahar zamani, domin tabbatar da cewa hukumar na da kwararrun shugabanni da za su jagoranci kirkire-kirkire da inganta ayyukan fasahar sadarwa a ciki da wajen jihar” in ji SSG.
Malam Bala Ibrahim ya ƙara da cewa an zaɓi waɗanda aka naɗa ne bisa cancanta, ƙwarewa, da nagarta.
Ya bukaci dukkan waɗanda aka naɗa da su yi aiki tukuru don aiwatar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati bisa kyakkyawan.
Sanarwar ta ƙara da cewa, dukkan waɗannan nade-naden sun fara aiki ne nan take.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Fasahar Sadarwa Jigawa fasahar sadarwa Jihar Jigawa daga Jami ar
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
Shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kano, Alhaji Salim Hashim Idris Gwangwazo, ya kaddamar da shirin kula da ido kyauta domin tallafawa jama’a da ke fama da ‘Glaucoma’ da ke lalata rijiyoyin ido, da ‘Cataract’ wato yanar ido da sauran cututtukan ido.
An gudanar da shirin ne a Asibitin Kwalli tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, da Hukumar Lafiyar Farko ta Jiha, da ƙaramar hukumar da masu bada tallafi daga kasashen waje.
Shirin ya haɗa da gwaje-gwajen lafiyar ido, da bayar da magunguna da kuma rarraba tabarau kyauta, musamman ga marasa ƙarfi a cikin al’umma.
Shugaban ƙaramar hukumar, ta bakin Kwamishinan Lafiya Alhaji Mustapha Darma, ya bukaci jama’a da su ci gaba da tallafawa gwamnati wajen samar da ingantaccen kulawa.
A baya-bayan nan, gwamnatin jihar ta dauki nauyin kula da lafiyar ido ga mutum sama da 500 daga Birnin Kano da sauran kananan hukumomi.
Shugaban kula da lafiya am matakin farko na ƙaramar hukumar, Alhaji Lawan Jafar, ya ce wadanda lalurar su ba ta tsananta ba za a ba su shawarwarin kula da lafiyar su, da magunguna, wa su ma har da tabarau, yayin da wadanda ta su ta tsananta kuma za a musu tiyata.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana sun nuna godiya tare da yi wa gwamnati addu’a don samun nasara.
Shugaban tawagar likitocin, Dr. Kamal Saleh, ya tabbatar da cewa shirin ya samu nasara sosai.
Daga Khadijah Aliyu