Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da nadin Dr. Mohammed Hassan a matsayin Darakta Janar na farko na Hukumar Fasahar Sadarwa da inganta Tattalin Arzikin ta fasahar zamani ta Jihar Jigawa.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya fitar a Dutse.

Kafin nadin nasa, Dr. Muhammad Hassan shi ne shugaban hukumar Fasahar Sadarwa da Kimiyya ta Jigawa, wato Galaxy ITT.

Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa sabo  shugaban hukumar ya sami digirinsa na farko a fannin Lissafi daga Jami’ar Bayero, Kano, a shekarar 2008. Daga bisani, ya samu digiri na biyu a fannin Kimiyyar Kwamfuta daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Afirka (AUST), Abuja, a shekarar 2011, sannan ya ci gaba da karatu har ya samu digirin digirgir (Ph.D) a fannin Kimiyyar Kwamfuta da Injiniyanci daga Jami’ar Aizu da ke kasar Japan, a 2018.

Haka nan, Gwamnan ya amince da naɗin Baffajo Beita a matsayin sabon shugaban Galaxy ITT.

Kafin naɗinsa, Beita  Babban Jami’in Bayanan Fasaha ne a Galaxy Backbone da ke Abuja. Yana da ƙwarewa mai zurfi a fannin fasahar sadarwa, musamman a tsarin gudanar da cibiyoyin sadarwa, tsaro na yanar gizo, da ƙirƙirar fasahar yanar gizo.

Beita ya kammala digirinsa na farko a fannin Kwamfuta daga Jami’ar Anglia Ruskin, kuma ya fara aikinsa ne a Makarantar Informatics ta Jihar Jigawa da ke Kazaure, kafin ya taka muhimmiyar rawa a manyan ayyukan fasahar sadarwa a Turai, Gabas ta Tsakiya, da Afirka (EMEA) a fannoni daban-daban, ciki har da masana’antar mai da gas, da sarrafa kayayyaki, da harkokin kuɗi”.

Bugu da ƙari, Gwamnan ya amince da naɗin Muhammad Nura Zubairu a matsayin Daraktan Zartarwa na Ayyukan Fasaha, da Umar Ibrahim Gumel a matsayin Daraktan Zartarwa na Harkokin Kasuwanci a  Galaxy ITT.

Kafin wannan matsayi, Muhammad Nura ya kasance Injiniyan Tallafin Sadarwa a Galaxy ITT, kuma ya kammala babbar difloma (HND) a fannin Tattalin Arzikin Hadin Gwiwa da Gudanarwa daga Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010.

“Wadannan muhimman nade-nade na cikin shirye-shiryen Gwamna Namadi na ƙarfafa tattalin arzikin  Jihar Jigawa ta fasahar zamani, domin tabbatar da cewa hukumar na da kwararrun shugabanni da za su jagoranci kirkire-kirkire da inganta ayyukan fasahar sadarwa  a ciki da wajen jihar” in ji SSG.

Malam Bala Ibrahim ya ƙara da cewa an zaɓi waɗanda aka naɗa ne bisa cancanta, ƙwarewa, da nagarta.

Ya bukaci dukkan waɗanda aka naɗa da su yi aiki tukuru don aiwatar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati bisa kyakkyawan.

Sanarwar ta ƙara da cewa, dukkan waɗannan nade-naden sun fara aiki ne nan take.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Fasahar Sadarwa Jigawa fasahar sadarwa Jihar Jigawa daga Jami ar

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran

Tawagar jami’ai da ‘yan kasuwan kasar Tunisiya ta gana da mataimakin shugaban kasar Iran

A yayin ganawarsa da ministan kasuwanci da fitar da kayayyaki na kasar Tunisiya Samir Ben Salem Obeid, mataimakin shugaban kasar Iran na farko na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: Lokaci ya yi da za a dauki kwararan matakai wajen fadada dangantakar tattalin arziki tsakanin Iran da Tunusiya.

A yayin taron, wanda aka gudanar a ofishinsa tare da halartar jakadan kasar Tunisiya a Iran Imed Rahmouni da tawagar da ke tare da shi, Aref ya bayyana cewa, dangantakar siyasa da ke tsakanin al’ummar Iran da Tunisiya na tafiya cikin wani yanayi mai ma’ana, amma hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ya kasance kasa da abin da ake bukata, bisa la’akari da dama da karfin da bangarorin biyu ke da shi.

A yayin ganawar, Aref ya tunatar da ziyarar da ya kai birnin Qairawan na kasar Tunusiya shekaru ashirin da suka gabata, lokacin da ya rike mukamin mataimakin shugaban kasar na farko na Jamhuriyar. Ya kara da cewa a lokacin yana jin kamar ya ratsa daya daga cikin garuruwan Khorasan na kasar Iran, yana daukar birnin Qairawan wata alama ce ta hadin kan al’ummar musulmi da alakar al’adu da addini tsakanin Iran da Tunisiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Ayyukan Sadarwa
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa