Madatsar Tiga Za Ta Samar Da Ruwan Sha A Garin Rano
Published: 3rd, April 2025 GMT
A kokarin magance matsalar karancin ruwan sha da garin Rano ke fuskanta na tsawon shekaru, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umarci Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da ta fara amfani da Madatsar Tiga don samar da ruwa mai a garin.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Dr.
Gwamna Yusuf ya yaba wa Sarkin Rano bisa jajircewarsa wajen kare muradun al’ummarsa, inda ya tabbatar masa da cewa gwamnati na daukar matakan da suka dace domin shawo kan matsalar ruwa a garin.
Ya bayyana cewa an riga an tsara shirin gina rijiyoyin burtsatse tare da hadin gwiwar ƙaramar hukumar, duk da cewa duwatsu da ke karkashin kasa na kawowa aikin cikas.
A kwanan nan ne gwamnatin jihar Kano ta gudanar da bincike domin tabbatar da lafiyar Madatsar ta Tiga, wacce za ta rika samar da ruwa a garin na Rano.
Haka kuma, madatsar tana dauke da tashar samar da wutar lantarki mai nauyin megawatt 10, wacce aka kammala gina ta a shekarar 2023.
Gwamna Yusuf ya nanata kudirin gwamnatinsa na ci gaba da inganta bangarori da dama, ciki har da noma, kiwon lafiya, muhalli, ilimi, da kuma karfafawa mata da matasa.
A nasa bangaren, Sarkin Rano, Ambasada Dr. Muhammad Isa Umar, ya gode wa Gwamna Yusuf bisa ci gaban da ake samu a masarautar, tare da rokon sa da ya ci gaba da mayar da hankali kan matsalar samar da ruwa.
Sarkin ya kuma yaba wa gwamnan bisa daukar mataki kan koke-koke da aka gabatar game da aikin titi mai nisan kilomita biyar, wanda hakan ya kai ga nusanya dan kwangilar da ya kasa yin aikin da wani wanda ya fi kwarewa.
Ziyarar gaisuwar Sallah ta kasance mai kayatarwa, inda aka gudanar da wasanni na gargajiya, ciki har da shahararrun mawakan garaya na Masarautar Rano, waɗanda suka nishadantar da jama’a.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Rano Ruwan Sha samar da ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
Kakakin ma’aikatar sharia a nan JMI ya bada sanarwan cewa,ma’aikatar za ta bayyanawa mutanen sakamakon bincken da suka gudanar kuma suke ci gaba da yi, dangane da fashewa da kuma gobatar da ta tashi a tashar jiragen ruwa ta Shahid Rajaee a cikin yan kwanakin da suka gabata. .
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran, ya bayyana cewa, Asgar Jahangir kakakin ma’aikatar sharia da kuma Zabihullah Khudayiyan shugaban hukumar bincike ta kasa, sun gudanar da taron hadin guiwa da yan jaridu da kafafen yada labarai na cikin gida da waje a safiyar, dangane da fashewa da kuma gobarar da ta biyo baya a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajaee.
Banda haka jami’an sun amsa tambayoyin yan jarida bayan jawabansu dangane da hatsarin wanda ya lakume rayukan mutane, fiye da 70 da kuma jikata wasu kimani dubu guda.
Kafin haka dai jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaee ya bada umurni ga ma’aikatun biyu su gudanar da cikekken bincike don gani musabbabin wannan hatsarin sannan idan akwai wadanda suka da hannu, ko sakaci a cikinsa, a bi tsarin da ake da shi don hukunta wadanda suke da laifi.