Madatsar Tiga Za Ta Samar Da Ruwan Sha A Garin Rano
Published: 3rd, April 2025 GMT
A kokarin magance matsalar karancin ruwan sha da garin Rano ke fuskanta na tsawon shekaru, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umarci Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da ta fara amfani da Madatsar Tiga don samar da ruwa mai a garin.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Dr.
Gwamna Yusuf ya yaba wa Sarkin Rano bisa jajircewarsa wajen kare muradun al’ummarsa, inda ya tabbatar masa da cewa gwamnati na daukar matakan da suka dace domin shawo kan matsalar ruwa a garin.
Ya bayyana cewa an riga an tsara shirin gina rijiyoyin burtsatse tare da hadin gwiwar ƙaramar hukumar, duk da cewa duwatsu da ke karkashin kasa na kawowa aikin cikas.
A kwanan nan ne gwamnatin jihar Kano ta gudanar da bincike domin tabbatar da lafiyar Madatsar ta Tiga, wacce za ta rika samar da ruwa a garin na Rano.
Haka kuma, madatsar tana dauke da tashar samar da wutar lantarki mai nauyin megawatt 10, wacce aka kammala gina ta a shekarar 2023.
Gwamna Yusuf ya nanata kudirin gwamnatinsa na ci gaba da inganta bangarori da dama, ciki har da noma, kiwon lafiya, muhalli, ilimi, da kuma karfafawa mata da matasa.
A nasa bangaren, Sarkin Rano, Ambasada Dr. Muhammad Isa Umar, ya gode wa Gwamna Yusuf bisa ci gaban da ake samu a masarautar, tare da rokon sa da ya ci gaba da mayar da hankali kan matsalar samar da ruwa.
Sarkin ya kuma yaba wa gwamnan bisa daukar mataki kan koke-koke da aka gabatar game da aikin titi mai nisan kilomita biyar, wanda hakan ya kai ga nusanya dan kwangilar da ya kasa yin aikin da wani wanda ya fi kwarewa.
Ziyarar gaisuwar Sallah ta kasance mai kayatarwa, inda aka gudanar da wasanni na gargajiya, ciki har da shahararrun mawakan garaya na Masarautar Rano, waɗanda suka nishadantar da jama’a.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Rano Ruwan Sha samar da ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
An yi kira ga manoma a jihar Kwara da su yi taka tsan-tsan domin hasashen za a samu ruwan sama da kuma tsawa da ake hasashen nan da kwanaki masu zuwa.
A wata sanarwa da kwamishinan noma da raya karkara na jihar, Dr, Afees Abolore ya fitar, ya ce a cewar hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet, ana sa ran wasu sassa na jihar za su fuskanci ruwan sama da kuma yiwuwar tsawa.
Ya ce za a fuskanci ruwan sama ne da rana da yamma, tsakanin Litinin 28 ga Yuli da Laraba 30 ga Yuli, 2025.
Ya yi bayanin cewa duk da cewa ba a sami ruwan sama ba tukuna, yanayin da ke gaba zai iya kawo cikas ga ayyukan noma da ake ci gaba da yi, musamman ga masu sharefilaye, da watsin taki, ko girbin amfanin gona.
Ya yi nuni da cewa wuraren da ke da ƙarancin magudanar ruwa ko kuma waɗanda ke kusa da hanyoyin ruwa na iya zama mafi haɗari ga ambaliya.
Sanarwar ta shawarci manoman da su daina amfani da takin zamani domin gujewa wankewa da almubazzaranci, da kuma girbi manyan amfanin gona da wuri domin hana lalacewa daga ruwan sama.
Yana ƙarfafa manoma da su ɗauki hasashen da gaske kuma su hanzarta yin aiki don rage cikas da kiyaye rayuwarsu.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU