Gwamnatin jihar Kwara ta kaddamar da wani shiri na sauya fasalin noma domin habbaka kiwon dabbobi da bunƙasa yankunan karkara a fadin jihar.

Jami’in shiri na musamman kan harkar noma wato Special Agro Industrial Processing Zone (SAPZ) a turance, Dr. Busari Isiaka ne ya bayyana hakan ga manema labarai.

Ya ce wannan shiri ne da aka samar ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da Bankin Raya Musulunci (IsDB) na Saudiyya domin kafa ingantattun abubuwan more rayuwa ga masu zuba jari da manoma a fannin sarrafa nama da madara.

Dakta Isiaka, wanda ya jaddada muhimmancin wannan aiki, ya bayyana cewa wannan ne karon farko da wani gwamna mai ci ke jagorantar kwamitin da ke kula da irin wannan babban shiri.

Ya bayyana cewa aikin zai gudana na tsawon shekaru biyar, tare da haɗin gwiwar kuɗi daga gwamnatin jihar da Bankin Raya Musulunci (IsDB).

Dakta Isiaka ya nuna cewa jihar Kwara ta nuna jajircewarta ga shirin tun da wuri ta hanyar biyan kuɗin haɗin gwiwa cikin gaggawa, wanda hakan ya sa ta zama jihar ta farko da ta  kuɗaɗen da aka wajabta mata.

Ya jaddada cewa manufar wannan shiri shi ne inganta kayayyakin more rayuwa na fannin noma, musamman a ɓangaren kiwon dabbobi, tare da mayar da hankali kan inganta rayuwar al’ummomin karkara.

 

ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi

A kokarinsa na gano hakikanin dalilan da suka sa aka bayar da beli ga wani sanannen mai safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Dan Wawu, da aka ce an sako shi bisa umarnin Kwamishinan Sufuri na Kano, Ibrahim Ali Namadi, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da wani kwamiti na mutum takwas domin gudanar da bincike mai zurfi.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne ya kaddamar da kwamitin a madadin gwamnan.

An umurci kwamitin da ya gudanar da binciken cikin mako guda, domin gano hakikanin abin da ya faru da kuma ba da shawarwari kan matakin da ya dace a dauka.

Shugaban kwamitin shi ne Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Shari’a da Dokoki, Barista Aminu Hussaini, yayin da Mambobin kwamitin suka hada da Barista Hamza Haladu, Barista Hamza Nuhu Dantani, Darakta Janar na Hukumar Ayyuka na Musamman, Manjo Janar Muhammad Sani (rtd), Comrade Kabiru Dakata, da Farfesa Mamun Mustapha daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil.

Sauran mambobin sun hada da Alhaji Abdullahi Mahmud Umar, Kwamishina II na Hukumar Kula da Ma’aikata, da Hajiya Bilkisu Shehu Mai Mota, Babbar Sakatariya a Sashen Gudanarwa da Sauran Ayyuka na  ofishin Sakataren Gwamnatin .Jihar, wadda za ta rike matsayin Sakatariya ga kwamitin.

Gwamna Yusuf ya bayyana damuwarsa matuka kan zargin da ake yi, inda ya sake jaddada kudirinsa na yaki da safarar miyagun kwayoyi da duk wani nau’in barna a cikin al’umma.

Sakataren Gwamnatin Jihar ya bayyana kwarin gwiwarsa kan mambobin kwamitin, yana mai cewa an zabo su ne bisa cancanta, kwarewa, karsashi, da kuma kwarin gwiwar cewa za su gudanar da wannan aiki yadda ya kamata.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi
  • Taron ‘Kasashe biyu’ A Gefen Taron MDD A NewYork
  • Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo
  • Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
  • VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace