Aminiya:
2025-03-15@23:53:59 GMT

Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-Rufai

Published: 13th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, ya tabbatar da cewa ya bar jam’iyyar APC ne da sanin Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.

El-Rufa’i ya bayyana komawarsa jam’iyyar SDP a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja

Ya ce bai gamsu da yadda ake tafiyar da APC ba cikin shekaru biyu da suka gabata.

Yayin da yake zantawa da BBC Hausa, El-Rufa’i ya bayyana cewa ya sanar da Buhari kafin ya fice daga APC.

“Na faɗa masa game da shawarar da na yanke a ranar Juma’a. Ina yawan tuntuɓarsa kan harkokin siyasata,” in ji shi.

El-Rufa’i ya kuma tuna cewa lokacin da yake gwamna, ya taɓa miƙa wa Buhari jerin sunayen kwamishinonin da zai naɗa domin ya duba su, don tabbatar da cewa babu wanda ya taɓa zaginsa.

Da aka tambaye shi ko yana da shugabannin siyasa da yake bi, El-Rufa’i ya ce, “Ina da mutanen da nake tuntuɓa kafin na yanke hukunci, kuma Buhari shi ne na farko a cikinsu.”

Game da ko yana nadamar goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sai ya ce, “Ba na nadama, amma wasu abubuwa sun ba ni mamaki.

“Na goyi bayan Tinubu ne saboda wasu shugabannin Musulmi na Yarbawa sun faɗa min cewa an mayar da su saniyar ware a siyasa, kuma na yi imanin cewa dole a bai wa Kudancin Najeriya mulki domin yin adalci da daidaito.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari tsohon gwamna El Rufa i ya

এছাড়াও পড়ুন:

‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’

Shugaban Kasa, Bola Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ke yi, tana yi ne da nufin gyara makomar yara masu tasowa.

 

Yayin da yake jawabi ga kungiyar ‘Yan majalisa ta uku – wadda ya kasance cikin a Jamhuriya ta uku – da suka kai masa ziyara a fadarsa, Shugaba Tinubu ya ce a baya kasar na kashe kudaden yaran kasar da ba a kai ga haihuwarsa ba.

 

“Shekara 50 da suka gabata, Najeriya na kashe kudaden yaran da ba a kai ga haihuwarsu ba, tare da mayar da hankali kan man fetur wajen samun kudin shiga. Ba a yi wani tsari na tallafa wa yaran da za a haifa a gaba ba,” kamar yadda ya ce.

 

Shugaban ya kuma bayyana tarin matsalolin da ya fuskanta a farkon mulkinsa, musamman fannin tattalin arzikin da rayuwar jama’a.

 

“Mun fuskanci tarin kalubale a lokacin da na karbi mulki. Inda ba mu dauki matakai ba da yanzu kasar ta talauce, kuma ai hakkinmu ne mu kare tattalin arzikinmu daga rugujewa”, in ji Shugaba Tinubu.

 

To amma shugaban ya ce a yanzu kwalliya ta fara biyan kudin sabulu dangane da sauye-sauyen da gwamatinsa ta fara ɓullo da su.

 

“Amma a yau bayan shimfida mai kyau da muka yi, mun smau nasarar magance matsalolin da suka tunkaro kasarmu, a yanzu canjin kudi ya daidaita, farashin abinci na ci gaba da sauka, musamman a lokacin Ramadan, da yardar Allah wahalar ta zo karshe”, a cewar shugaban kasa.

 

Bello Wakili/Abuja

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba
  • Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC
  • Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
  • MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP
  • ‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’
  • 2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa
  • Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
  • Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai
  • Peter Obi ya kusa dawowa APC — Hadimin Tinubu