Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-Rufai
Published: 13th, March 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, ya tabbatar da cewa ya bar jam’iyyar APC ne da sanin Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.
El-Rufa’i ya bayyana komawarsa jam’iyyar SDP a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a AbujaYa ce bai gamsu da yadda ake tafiyar da APC ba cikin shekaru biyu da suka gabata.
Yayin da yake zantawa da BBC Hausa, El-Rufa’i ya bayyana cewa ya sanar da Buhari kafin ya fice daga APC.
“Na faɗa masa game da shawarar da na yanke a ranar Juma’a. Ina yawan tuntuɓarsa kan harkokin siyasata,” in ji shi.
El-Rufa’i ya kuma tuna cewa lokacin da yake gwamna, ya taɓa miƙa wa Buhari jerin sunayen kwamishinonin da zai naɗa domin ya duba su, don tabbatar da cewa babu wanda ya taɓa zaginsa.
Da aka tambaye shi ko yana da shugabannin siyasa da yake bi, El-Rufa’i ya ce, “Ina da mutanen da nake tuntuɓa kafin na yanke hukunci, kuma Buhari shi ne na farko a cikinsu.”
Game da ko yana nadamar goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sai ya ce, “Ba na nadama, amma wasu abubuwa sun ba ni mamaki.
“Na goyi bayan Tinubu ne saboda wasu shugabannin Musulmi na Yarbawa sun faɗa min cewa an mayar da su saniyar ware a siyasa, kuma na yi imanin cewa dole a bai wa Kudancin Najeriya mulki domin yin adalci da daidaito.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Buhari tsohon gwamna El Rufa i ya
এছাড়াও পড়ুন:
DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Tatsuniya wata hanya ce ta ilmantarwa da bayar da tarbiyya da kuma koyar da al’adu da halaye na gari a tsakanin Hausawa.
Tatsuniyoyi na ɗauke da darussa na rayuwa, suna kuma koya wa yara da manya jarumta da tausayi da sauran dabi’u kyawawa.
Sai dai a yayin da duniya take sauyawa, ba kasafai matasa suke sha’awar sauraron tatsuniya ba.
NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaWannan ne batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan