Aminiya:
2025-11-18@12:51:33 GMT

Boko Haram ya wuce yadda mutane ke tsammani — Jonathan

Published: 3rd, October 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce Boko Haram sun fi sojojin Najeriya makamai, lamarin da ya sa yaƙin ya zama ɗaya daga cikin manyan matsalolin tsaron ƙasar nan.

Ya bayyana haka ne a Abuja lokacin ƙaddamar da littafin Scars: Nigeria’s Journey and the Boko Haram Conundrum da tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor (mai ritaya), ya rubuta.

2027: Dalilin da ya sa Atiku bai ayyana takararsa ba — Hadimi Fashewar tukunyar gas ya haddasa gobara a jami’ar Gombe

Jonathan, ya ce rikicin Boko Haram ya bambanta da sauran matsalolin da Najeriya ta fuskanta kamar na ’yan tawayen yankin Neja Delta da rikicin addini ko ƙabilanci.

Ya bayyana cewa Boko Haram sun samu goyon baya daga ƙasashen waje, suna da aƙidar tsattsauran ra’ayi da kuma makamai na zamani, abin da ya tsananta rikicin.

“Boko Haram ta fi yadda mutane ke tunani. A wani lokaci, mayaƙansu sun fi sojojinmu makamai, abin da ya nuna akwai ƙungiyoyin ƙasashen waje da ke tallafa musu,” in ji Jonathan.

Ya ƙara da cewa sace ’yan matan Chibok da suka yi a 2014 ya kasance ɗaya daga cikin abubuwan da suka fi baƙanta masa rai a lokacin shugabancinsa.

Jonathan ya kuma tuna yadda ya tunkari ’yan tawayen Neja Delta a lokacin da yake Mataimakin Shugaban Ƙasa.

Ya ce ya ziyarci sansanoninsu ba tare da  tsaro ba, saboda ya yi imani cewa tattaunawa tare da amfani da ƙarfin soja ne zai kawo zaman lafiya.

Wannan dabara, a cewarsa, ta taimaka wajen wanzar da zaman lafiya a yankin.

Amma ya jaddada cewar rikicin Boko Haram ya bambanta.

Ya ce idan son kawo ƙarshen Boko Haram, dole ne Najeriya ta haɗa matakan soja da kyakkyawan tsari  shugabanci, rage talauci, tallafa wa matasa, da adalci.

“Ba za mu ɗauki Boko Haram kawai a matsayin matsalar tsaro ba. Tushenta talauci ne, da wariya. Sai an yi aiki gaba ɗaya kafin a samu zaman lafiya na gaskiya,” in ji shi.

Jonathan ya kuma yaba wa Janar Irabor bisa rubuta littafin, inda ya bayyana cewa zai taimaka wa al’umma su fahimci rikicin Boko Haram sosai, ya kuma zama jagora ga shugabannin gaba.

Taron ya samu halartar fitattun mutane ciki har da tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, tsohon Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Babagana Monguno, Hafsoshin Tsaro, Ministoci, Jakadu, da kuma Sarakunan Gargajiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Babban lauya kuma mai kare haƙƙin ɗan Adam, Femi Falana (SAN), ya bai wa ƴan Nijeriya shawara da su kai Gwamnatin Tarayya ƙara don neman a mayar musu da kuɗin fansar da suka biya yayin da aka yi garkuwa da ƴan uwansu. Ya ce gwamnatin ta kasa sauke babban nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata na kare rayuka da dukiyoyin ƴan ƙasa.

Falana ya yi wannan jawabi ne a lokacin buɗe sabuwar shekarar Shari’a ta Tsangayar Shari’a ta Jami’ar Yakubu Gowon da ke Abuja. Ya ce yawaitar garkuwa da mutane a sassan ƙasar nan ya nuna gazawar gwamnati wajen tabbatar da kariya kamar yadda kundin tsarin mulki da Yarjejeniyar Afrika kan Haƙƙin Dan Adam suka tanada. Ya kuma soki bambancin yadda hukumomi ke tunkarar lamarin, yana mai cewa ana hanzari ne idan manyan mutane aka sace, amma an bar talakawa cikin tsoro da halin ƙaƙa-niki-ka-yi.

Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Falana ya jaddada cewa kai gwamnati kotu zai taimaka wajen kare haƙƙin waɗanda suka biya kuɗin fansa, tare da matsa wa gwamnati ta inganta tsaro cikin gaggawa. Sabon rahoton Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ya nuna cewa ƴan Nijeriya sun biya Naira Tiriliyan 2.23 a matsayin kuɗin fansa tsakanin Mayu 2023 zuwa Afrilu 2024. Rahoton Crime Experience and Security Perception Survey (CESPS) na 2024 ma ya nuna cewa fiye da mutum miliyan 2.2 an yi garkuwa da su a wannan lokaci, tare da matsakaicin kuɗin fansa na kusan ₦2.7m ga kowane mutum.

ADVERTISEMENT

A cewar masana tsaro, garkuwa da mutane ya koma kasuwancin da ke samar da riba ga miyagu, lamarin da ke buƙatar tsauraran matakai daga gwamnati tare da ingantaccen tsari da haɗin gwuiwar jami’an tsaro.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara November 16, 2025 Manyan Labarai Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle November 16, 2025 Nazari Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna? November 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PDP Ba Ta Mutu Ba Duk Da Rikicin Da Ta Ke Fama Da Shi – Anyanwu
  • Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang
  • Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya
  • Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa
  •  An Bayyana Sunayen Kasashen Da Su Fi Sayarwa “Isra’ila” Man Fetur A Lokacin Yakin Gaza
  • Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba
  • Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso
  • Yadda Za Ku Gyara Kanku