Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi
Published: 3rd, October 2025 GMT
Kudubi yana tare da kwayar zarrar kowace halittar Allah, shi yake isar mata da sakon magana, wanda bai zauna da wadannan mazaje ba sai ya ji magana ce mai girma, sai ya ga kamar an maida shi Allah, ya ce mai aka bar wa Allah ragowa, abun ba haka yake ba, abun mammaki da mai fadar wannan yana da wayewar da yake ganin fina-finai na Turawa, da ya ga wannan magana kai-tsaye a sarari.
Misali a kan Kudubi, Turawa suna da wani fim da suke shiryawa na Dirakula (Dracula) wani mai shan jini, abun kamar tatsuniya ce suke shiryawa, amma wani ya ce an yi fada ne da Daular Usmaniyya, wato daular Turkiya, akwai abubuwa da ya ba su tsoro sai suka maida wannan daular ta zamo daular da ke shan jini, amma ainihi wani sarki ne daga cikn daular Usmaniyya, amma ba haka abin yake ba, kila walitta yake nuna masu, kila wani abu ya nuna masu. Muhimmin abin da nake son in fada idan a wannan fim din wannan shu’umi (actor) ya sha jini ko ya ba wani jininsa (to wannan jini na Dirakula shi ne Kudubi), su da shi ke ba su san Allah ba, shi ya sa suka kawo misali da jinin jikin mutane, to duk wanda mutumin da ya sha sai ya rika jin duk wani motsi da halittar Allah, haka nan da sauro zai kada fukafukansa a karshen duniya da zai ji a kunnensa, wannan kenan.
Turawa suka shirya, kar ka ga ba su da addini, kwarewa ko sani cikin wadannan abubuwa. A’a suna da shi, suna da addini da malamai suna da Falsafofi, suna da Ruhubanai da kullum suke a cikin halwa. Idan kana bin irin wadannan fina-finai za ka ga abubuwan mamaki.
Akwai wani fim da kasar Ingila ta shirya na ‘The Seeker”, Falillahi, idan za ka kawo misali koda waye ka kawo muddin za a fahimci ilimi, Allah zai iya buga misali da sauro ko gizo-gizo, kafirai suka ce kuma misali ya kare da ake buga misali da sauro. Allah ba ya jin kunyar buga msali da komai, don haka nan mu ma za mu kawo don mu fahimci ilimi ba mu tsoron buga misali da The Seeker da Merlin da sauransu.
Yanzu wannan The Seeker din, idan ka lura yadda suka shirya fim din, shi Kudubi ne mai zaman kansa, amma shi kansa bai san kansa ba, shi kuma yana da wasu masu kiyayeshi, yana da wani kudubi Zaitu wanda shi ya san waye wannan, shi ya san sigar nan, kuma kiyaye shi yana hannun Zaitun nan, Allah ya hada shi da wasu mata, akwai wata ta iya tarbiyyantarwa, akwai wata Sufiya da duk wasu Kuduai ba su da tasiri a kanta, wannan abu duk akwai shi. Shehu Tijjanin Abul Abass (RTA), ya ce yafi mafatihul Kunuzi ta wani wajen su kuma sun fi shi ta wani wajen.
Sayyidina Kabiru ya za ci ya san duk Waliyyan Allah, sai da ya je Baitul Mukaddasi ya ga Abdulrazaki mutane sun kewaye shi yana ba da karatu, sai ya ga wani yaro a kwance yana bacci, sai ya zo ya yatshi yaro ya ce kai ba ka jin kunya duk mutane suna wajen Abdulrazaki suna karatu, sai ya ce ka kyale ni malam, ni wajen Razzaku nake karatu, mu ba a wajen bawan Razzaku muke ba, a wajen Razzaku muke karatu, sai ya ce yi kwanciyarka, sai ya ga cewa akwai aiki a gabansa.
To a cikin wannan fim din, akwai wata kalma da Zaitu yake fada wa wata mata da yake tafiya da ita, ya ce ki duba yau mu ne muradin Allah a kan kasa, Allah mu yake kallo a kan kasa, mu Allah ke nufi a kan kasa amma kuma ko gida ba mu da shi a doran kasa a daji muke yawo, wannan ya nuna cewa ba wai don kana waliyi shi kenan kai dan mai da nono ne, kai sai kaza da kaza ba.
Yayin da yake tafiya da wannan yaro, duk da ya dame su, sai ya ce ke wannan yaro da kike gani shi ne duniya gaba daya, wani ruhi ne, idan wannan yaro ya rushe shikenan duniya ta kare, duniya fanko ce, wannan yaro shi ne duniya.
Ilimin walitakka, ba wani ilimi ne sabo da aka kago ba , ilimi ne da dama yana nan tun farko, duk malamai masu hikima masu halwa suna nan da shi, akwai wani matsayi da Waliyi yake hawa, ya na samu ne daga zikiri da halwa da tunani da abin da Allah ya rubuta masu suke kaiwa wannan matsayi, suna jin halittar Allah kaf da kunnensu kuma wannan ba ta kare masu jin wancan ba, ba ta shagaltar da shi wancan ba, kuma yana harkokinsa na rayuwa yana baccinsa yana aurensa, kaga wannan ya fi karfin hankali, wannan Kudubi ke da irin wannan.
Sayyadi Ali, Allah ya kara masa yarda, shi ke maganar walitta, shi ne asalin Sufaye gaba daya, sunansa waliyi waliyen muminai wata rana yana kan hanyarsa ta zuwa yakI sai ya zo shigewa ta wajen da Annabi Sulaiman ya shige watau wadil Namli, daji ne na tururuwai, Salmanul Farisi ya kalli dajin bakikirin sai tururuwai, sai ya ce tsarki ya tabbata ga Allah wanda ya halicci wadannan tururuwai kuma ya san adadinsu, sai Sayyadi Ali ya ce, zo in koya ma tasbihi baka iya tasbihi ba, ka ce tsarki ya tabbata ga Allah da Ya halicci wadannan tururuwai, amma wasu bayin Allah sun san adadinsu, ka gan ni nan, na san adadinsu, na san mata a cikinsu na san kuma san maza, haka nan kuma na san masu kwai na san marasa kwai.
Shehu Tijjani Abul Abassi, ya ce idan har Kudubi ya zama haka wanda shi kuma tsakaninsa da Annabi kamar yadda tururuwa take da tafiyar shaho a sama, shi Annabi shi shi ne kamar mai tafiyar shaho a sama (wato saurin tafiyar), shi kuma Kudubi shi yake daidai da tafiyar tururuwa a kasa (wajen yanayin sauri) haka nan ganinsa da na Annabi duk da wannan tsarki na Kudubi, to mun gode wa Allah, Manzon Allah (SAW) shi ne Annabin annabawa, malamin malamai.
Za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wannan yaro
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’ariv: Netanyahu Yana Tsoron Hukuncin Da Kotu Za Ta Yanke Akansa
Jaridar “ma’ariv’ ta buga labarin dake cewa Fira minista Netanyahu yana rayuwa cikin zullumi da tsoro mai tsanani akan hukuncin da kotu za ta yanke masa.
Jaridar ta ‘yan sahayoniya ta kuma ce yadda ake yin matsin lamba daga waje domin ganin an yafe wa Netanyahu,yana nuni ne da yadda Fira ministan yake cikin tsoro da razana akan hukuncin da kotun za ta yanke a kansa.
Kwanaki kadan da su ka gabata ne dai shugaban kasar Amurka ya aike da wasika zuwa ga shugaban Haramtacciyar kasar Isra’ila Ishaq,,, yana bukatar ya yi wa Netanyahu afuwa.
Ana tuhumar Netanyahu ne daaii da cin hanci da rashawa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Bayyana Sunayen Kasashen Da Su Fi Sayarwa “Isra’ila” Man Fetur A Lokacin Yakin Gaza November 15, 2025 MDD: Mutane 100,000 Ne Su Ka Fice Daga Birnin Al-Fasher Na Kasar Sudan November 15, 2025 Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Yace Iran Ba za Ta Taba Mika Wuya Ga Duk Wata Barazana Ba November 15, 2025 Kasashen Latin Amurka Sun Shirya Tsaf Don Mayar Da Martani Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Kan Venuzuwela November 15, 2025 Rasha Tace Bata Da Shirin Kai wa Kungiyar Nato Hari Amma Za ta Mayar Da Martani Kan Duk Wata Barazana November 15, 2025 Shugaban Iran Da Prime Ministan Iraqi Sun Tattaunawa Kan Batun Zabe Da Kuma Alakar Dake Tsakaninsu. November 15, 2025 M D D Ta yi Tir Da Harin Da Yahudawa Yan Share Wuri Zauna Suka Kai A Masallaci A Yammacin kogin Jodan November 15, 2025 Mali ta Dakatar da Tashoshin Talabijin na Faransa TF1 da LCI November 15, 2025 Gaza: Amurka na matsin lamba ga kwamitin tsaro don amincewa da shirin Trump November 15, 2025 AU da MDD, sun karfafa dabarun tabbatar da zaman lafiya da tsaro November 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci