Kakakin majalisar Kano Ya Yi Murnar Cikar Najeriya Shekaru 65
Published: 2nd, October 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Alhaji Jibril Ismail Falgore, ya mika sakon taya murna ga ‘yan Najeriya a daidai lokacin da kasar ke cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Kamaluddeen Sani Shawai ya fitar, shugaban majalisar ya bayyana tafiyar Najeriya bayan samun ‘yancin kai a matsayin wanda ke cike da kalubale da dama, yana mai cewa idan aka yi hangen nesa da tsare-tsare, makoma mai haske tana nan kusa.
Ya lura cewa duk da matsaloli, Najeriya a yau tana tsaye a matsayin kasa mai mutane sama da miliyan 230, galibi matasa da kuzarin da ke da karfi na musamman da kasashe da yawa ba su da su.
“A nan Jihar Kano, Majalisar ta tsaya tsayin daka wajen aiwatar da ayyukanta na doka da sa ido, ba tare da la’akari da cin hanci da rashawa ba, da kuma kudurin inganta rayuwar al’ummarmu.
A madadin majalisar dokokin jihar Kano, Falgore ya mika sakon taya murna ga gwamna Abba Kabir Yusuf, da al’ummar jihar Kano, da daukacin ‘yan Najeriya.
Rel/Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
AU ta sake nanata cewa “Babu kisan kare dangi a arewacin Najeriya
Shugaban Kwamitin Tarayyar Afirka ya yi watsi da zargin da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi cewa ana wa Kiristoci kisan kare dangi a arewacin Najeriya.
Da yake jawabi a wani taron Majalisar Dinkin Duniya a New York, ya ce irin wadannan kalamai kan iya gurbata matsalolin tsaro mai sarkakiya.
Da yake magana tare da Sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres a ranar Alhamis, Mahmoud Ali Youssouf ya jaddada cewa Tarayyar Afirka ta riga ta fayyace matsayinta kuma ta yi kira da a yi taka tsantsan a cikin harshen da ake amfani da shi wajen bayyana rikice-rikicen da ke faruwa a nahiyar.
“Babu kisan kare dangi a arewacin Najeriya,” in ji Youssouf. “Mun fitar da wata sanarwa a fili da ke nuna cewa abin da ke faruwa a arewacin Najeriya ba shi da alaka da ta’addancin da muke gani a Sudan ko a wasu sassan gabashin DRC.”
Musulmai da Kiristoci, dukkansu abin ya shafa inji shi…
Ya kara da cewa tashin hankalin da ake yi a arewacin Najeriya, wanda galibi kungiyoyin ta’addanci na Boko Haram da ISIS a Yammacin Afirka ke haifarwa, ya shafi Musulmai da Kiristoci.
“Ina ganin lamarin arewacin Najeriya ya kamata mu yi taka tsantsan kafin mu yi irin wadannan kalamai,” in ji Youssouf.
“Musulmai ne suka fara shan wahala a hannun Boko Haram, ba Kiristoci ba, kuma ina faɗin haka ne bisa bayanai da muke dasu.”
A kwanan baya ne shugaba Trump na Amurka ya bayyana cewa zai doki matakin soji a Najeriya bisa zargin cewa gwamnatin kasar na kauda kai a game da kisan da y ace ana wa Kiristoci a kasar batun da Najeriya ta musanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Falasdinu ta yi wasan sada zumunci a Spain November 16, 2025 Amurka Ta Yi Gwajin Makaman Nukiliya A Watan Ogusta November 15, 2025 Adadin Ma’adanin “Colbat” Da DRC Ta Bai Wa Duniya Ya Kai Ton 1,000 November 15, 2025 Ma’ariv: Netanyahu Yana Tsoron Hukuncin Da Kotu Za Ta Yanke Akansa November 15, 2025 An Bayyana Sunayen Kasashen Da Su Ka Fi Sayar Wa “Isra’ila” Man Fetur A Lokacin Yakin Gaza November 15, 2025 MDD: Mutane 100,000 Ne Su Ka Fice Daga Birnin Al-Fasher Na Kasar Sudan November 15, 2025 Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Yace Iran Ba za Ta Taba Mika Wuya Ga Duk Wata Barazana Ba November 15, 2025 Kasashen Latin Amurka Sun Shirya Tsaf Don Mayar Da Martani Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Kan Venuzuwela November 15, 2025 Rasha Tace Bata Da Shirin Kai wa Kungiyar Nato Hari Amma Za ta Mayar Da Martani Kan Duk Wata Barazana November 15, 2025 Shugaban Iran Da Prime Ministan Iraqi Sun Tattaunawa Kan Batun Zabe Da Kuma Alakar Dake Tsakaninsu. November 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci