Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-18@12:35:08 GMT

Gwamnan Jigawa Ya Taya Al’umma Murnar Samun ‘Yancin Kai

Published: 2nd, October 2025 GMT

Gwamnan Jigawa Ya Taya Al’umma Murnar Samun ‘Yancin Kai

Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa, ya taya gwamnati da al’ummar Nijeriya murnar cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai, inda ya bayyana ranar a matsayin abin tunawa da hadin kai, juriya, sadaukarwa da suka gina kasar.

 

A sakonsa na fatan alheri, Gwamna Namadi ya ce bikin ba wai kawai lokacin yin tunani ne kan irin gwagwarmayar da iyayen da suka kafa kasar suka yi ba, har ma wata dama ce ta sabunta sadaukarwar hadin gwiwa don samar da zaman lafiya, ci gaba, da wadata.

 

“A yau, muna bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai cikin alfahari da godiya. Wannan ranar tana tunatar da mu sadaukarwar da jaruman mu suka yi a baya, wadanda hangen nesa da jajircewarsu suka kafa tushen kasarmu mai kauna. A matsayinmu na al’umma, dole ne mu ci gaba da tabbatar da akidar hadin kai, adalci, da yiwa bil’adama hidima,” in ji gwamnan.

 

Malam Umar Namadi ya bayyana cewa, duk da kalubalen da Najeriya ke fuskanta, Najeriya na ci gaba da samun ci gaba a karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda manufofinsa ke da nasaba da karfafa tattalin arziki, inganta tsaro, da samar da damammaki ga ‘yan kasa.

 

A cewarsa, gwamnatinsa ta dukufa wajen ganin ta kara kaimi ga kokarin gwamnatin tarayya ta hanyar baiwa al’ummarmu fifiko, zuba jari a fannin noma, ilimi, kiwon lafiya, samar da ababen more rayuwa, da samar da damammaki ga matasa da mata.

 

“Tare, za mu gina kasa mai karfi da kuma ba da gudummawa ga daukakar Najeriya.”

 

Namadi ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa da hadin kai da kuma fata, yana mai jaddada cewa bambancin al’ummar kasa ne tushen karfi maimakon rarrabuwa.

 

Ya yi kira ga ‘yan kasa da su ci gaba da marawa manufofi da shirye-shiryen gwamnati goyon baya domin samun ci gaba mai dorewa.

 

“Yayin da muke daga tutarmu mai kore da fari a yau, bari mu tuna cewa alhakin gina Najeriya mai ci gaba ya rataya a kan mu baki daya. Tare da hadin kai, imani, da azama, za mu shawo kan kalubalen mu, mu cika burinmu na kasa mai girma”.

 

USMAN MZ/Dutse

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa murna

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce gwamnati ce ke da alhakin samar da tsaro da haɗin kai a Jihar Filato da kuma Najeriya baki ɗaya.

Ya ce babu wata ƙasa da za ta shigo don kawo zaman lafiya na dindindin a Najeriya, face ’yan ƙasa sun haɗa kai.

’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang

Akpabio, ya yi wannan magana ne a filin Polo na Jos a ranar Asabar yayin taron tarbar sabbin mambobin da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a Jihar Filato.

Ya kira jama’a da su goyi bayan ƙoƙarin samar da zaman lafiya tare da yin aiki don ƙarshen rikice-rikece.

Ya ce Shugaba Bola Tinubu yana ƙoƙarin kawo ƙarshen kashe-kashe da tabbatar da zaman lafiya a Filato da sauran sassan ƙasar nan.

“Muna roƙon Allah Ya taimaka mana mu samu zaman lafiya a Filato. Duk wanda zai mulki Filato dole ne ya zama mutum mai kishin zaman lafiya. Wannan ita ce jam’iyyar da ta ke kula da ku,” in ji shi.

Akpabio, ya ƙara da cewa: “Na zo a madadin Shugaban Ƙasa domin tabbatar muku cewa za mu yi duk abin da ya kamata domin ku samu zaman lafiya.

“Babu wasu mutane daga waje da za su zo su kawo muku zaman lafiya. Dole mu ne za mu samar da shi. Dole mu zauna lafiya da juna. Najeriya na buƙatar zaman lafiya domin samun ci gaba.”

Ya tabbatar wa al’ummar Jihar Filato cewa gwamnati za ta magance matsalolin da suke fuskanta.

“Ina kuka a duk lokacin da na ji an kashe wani mutum; yaro ko babba. Matsalar da muke fuskanta ba yau ta samo asali ba.

“Mutane da dama sun mutu a Filato. An zubar da jini mai yawa, kuma ba mu farin ciki da haka. Shugaban Ƙasa ma ba ya farin ciki,” in ji shi.

Akpabio ya amince cewa da cewar ana kashe-kashe, tashe-tashen hankula a ƙasar nan, amma ya yi alƙawarin cewa nan da wani lokaci lamarin zai zama tarihi.

Ya roƙi al’ummar Filato da su goyi bayan Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewar za su samar da ci gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon jami’an MDD Yayi Tir Da Amincewa Da Kudurin Amurka A Kwamitin Sulhu Kan Gaza
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar
  • Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
  • Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
  • Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
  • PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu