Li Qiang Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Sabon Firaministan Algeria
Published: 1st, October 2025 GMT
A jiya 30 ga watan Satumba, firaministan kasar Sin Li Qiang ya mika sakon taya murna ga Safi Kharib bisa zama sabon firaministan kasar Algeria.
Li Qiang ya bayyana cewa, Sin da Algeria sun sada zumunta mai zurfi da juna. A cikin shekaru 67 da kulla dangantakar diflomasiyya a tsakanin kasashen biyu, an raya dangantakarsu yadda ya kamata, da yin kokari tare da nuna goyon baya ga juna.
Sin ta maida hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Algeria, firaminista Li Qiang yana son yin kokari tare da firaminista Kharib wajen aiwatar da ayyukan da kasashen biyu suka cimma daidaito, da yin imani da juna, da zurfafa hadin gwiwa, don sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakanin kasashen biyu zuwa sabon matsayi. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: raya dangantakar Li Qiang ya
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ba za ta buga kofin duniya ba karo na biyu a jere
Jamhuriyar Congo ce za ta wakilci Afirka a sauran wasan cike gurbin shiga gasar kofin duniya, bayan da ta yi nasara a kan Najeriya da cin 4-3, bayan da suka tashi kunnen doki 1-1.
Congo za ta fafata da Bolivia da New Caledonia da Iraki da Jamaica da kuma Panama da za su kece raini a birnin Guadalajara da Monterrey a Mexico a watan Maris.
Super Eagles ta kai gasar kofin duniya shida daga bakwai tsakanin 1994 zuwa 2018, kuma wannan shi ne karon farko da Najeriya ba za ta buga kofin duniya ba karo biyu a jere tun 1990, bayan kasa zuwa 2022 a Qatar.
Wannan shi ne karon farko da Congo DR za ta je babbar gasar tamaula ta duniya da zarar ta samu gurbin, bayan 1974 a Jamus, amma a lokacin ana kiranta Zaire.
Za a buga gasar kofin duniya tsakanin tawaga 48 a Amurka da Canada da Mexico a 2026.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka DRC: An Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar M23 November 16, 2025 An Yi Kira A Bai Wa ‘Yan Hijira Saboda Sauyin Muhalli Kariya November 16, 2025 An Amince Da Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin November 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon November 16, 2025 Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya November 16, 2025 Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran November 16, 2025 Kanada Ta Tsare Tsohon Wakilin Majalisar Dinkin Duniya Mai Bincike Kan Laifukan Yakin Israila. November 16, 2025 Zarfi: HKI Ce Kawai Take Ayyana Nukiliya Ba Bisa Kaida Ba A Yammacin Asiya. November 16, 2025 Shugaban kasar venuzuwela Yayi Tir Da Atisayan Soji Da Trinidad and Tobago Ke yi. November 16, 2025 IRGC ta kama wani jirgin ruwan dakon mai a gabar tekun kudancin Makran November 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci