Leadership News Hausa:
2025-11-18@12:30:58 GMT

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Wanzar Da Zamanantarwa Irin Ta Sin

Published: 30th, September 2025 GMT

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Wanzar Da Zamanantarwa Irin Ta Sin

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira ga daukacin jama’ar kasar Sin da su yi aiki tukuru, tare da ingiza wanzar da zamanantarwa irin ta Sin. Xi, wanda kuma shi ne sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar zartarwar rundunar sojojin Sin, ya yi kiran ne yayin taron bikin cika shekaru 76 da kafuwar janhuriyar jama’ar kasar Sin, wanda ya gudana yau Talata a babban dakin taruwar jama’a dake birnin Beijing.

Shugaba Xi, ya jaddada cewa a gabar da yanayin harkokin duniya ke saurin sauyawa cikin sama da karni guda, dole ne a yi aiki tukuru wajen yayata akidun bai daya na dukkanin bil’adama, da aiwatar da tsarin cudanyar mabanbantan sassa, da ingiza aiwatar da shawarwarin bunkasa ci gaban duniya, da shawarwarin tsarin shugabancin duniya, da shawarwarin wayewar kan duniya, da shawarwarin shugabancin kasa da kasa, da aiki tare da dukkanin kasashe wajen gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama.

Kasar Sin tana gudanar da bikin ranar kafuwarta a ranar daya ga watan Oktoba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da shawarwarin

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya buƙaci al’umma su ƙara kula da tsaro tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, yayin da ’yan bindiga suka fara kai hare-hare a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina.

Sarkin, ya yi wannan kira ne yayin ziyarar jaje da ya kai wa al’ummar Faruruwa da ke Ƙaramar Hukumar Shanono a Jihar Kano.

Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16 Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang

A baya-bayan nan ’yan bindiga sun kai hari yankunan, inda suka sace shanu tare da yin garkuwa da mutane.

Sarki Sanusi, ya ce yawan hare-haren da ake fuskanta a yankin ya nuna cewa ana buƙatar kula da goyon bayan sarakunan gargajiya, gwamnati da kuma ƙungiyoyin sa-kai.

“Tsawon watanni da suka gabata, hare-hare sun ƙaru a ƙauyukan da ke iyaka da Jihar Katsina, inda ’yan bindiga ke zuwa su sace shanu, su kashe jama’a, su yi garkuwa da maza da mata,” in ji shi.

Ya ce ya kai ziyarar ne domin jajanta wa mazauna yankin da abin ya shafa, tare da tabbatar musu da goyon bayan gwamnati, da kuma ƙarfafa musu gwiwa su taka rawa wajen kare ƙauyukansu.

“Nauyinmu ne a matsayinmu na shugabanni mu zo mu ga mutanenmu, mu yi musu ta’aziyya, mu kuma tabbatar musu cewa gwamnati da jami’an tsaro suna yin iya bakin ƙoƙarinsu,” ya ce.

Sarkin ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta tura jami’an tsaro da kayan aiki don tsaron yankin.

“Gwamna ya sayi motocin aiki, ya samar da kayan aiki, kuma mutane na gani da idonsu yadda sojoji da ’yan sanda ke yawan sintiri a yankin.

“Muna kuma ƙarfafa musu gwiwa su yi amfani da ’yan sa-kai wajen kare ƙauyukansu,” a cewarsa.

Sarki Sanusi, ya kuma bukaci al’ummomin Katsina da ke maƙwabtaka da yankunan da su tabbatar cewa yarjejeniyar sulhu da suke yi da ’yan bindiga ba za ta zama silar kawowa Kano hari ba.

Ya yi addu’ar Allah Ya wanzae da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa, tare da alƙawarin ci gaba da aiki tare da gwamnatin jihar domin kare rayukan jama’a.

“Muna rokon Allah Ya dawo mana da zaman lafiya, kuma za mu ci gaba da yin iya bakin ƙoƙarinmu tare da gwamnati domin tabbatar da tsaro a wannan jiha,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda
  • An Yi Kira A Bai Wa ‘Yan Hijira Saboda Sauyin Muhalli
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30
  • Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya
  • Lebanon za ta shigar da kara a kan Isra’ila a MDD game da gina Katanga a iyakarta
  • Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 
  • Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin
  • Yadda Za Ku Gyara Kanku