Trump: Za mu goyi bayan Netanyahu idan Hamas ba ta amince da kudirinmu ba
Published: 30th, September 2025 GMT
Shugaban Amurka Donald Trump ya fada a wani taron manema labarai na hadin gwiwa tare da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a fadar White House jiya litinin cewa, yana fatan samun zaman lafiya mai dorewa a yankin gabas ta tsakiya.
Trump ya sanar da kaddamar da abin da ya kira “Ka’idojin Zaman Lafiya” a hukumance, tare da yin la’akari da abin da ya kira amincewar shugabannin kasashen Larabawa da na musulmi tare da tabbatar da goyon bayansu ga shirinsa na samar da mafita a zirin Gaza, in ji shi.
A cikin cikakkun bayanai kan shirin da Trump ya gabatar, za a saki dukkan fursunonin Isra’ila a zirin Gaza cikin sa’o’i 72 idan Hamas ta amince da shawarar. Shugaban na Amurka ya kuma bayyana cewa, shugabannin sun daura damara kan kawar da Hamas da kuma sauran kungiyoyi daga tafiyar lamarin Gaza bisa shirin da ya tsara.
Trump ya ce sojojin Isra’ila za su janye daga zirin a matakai, yana mai cewa “bangarorin za su amince da jadawalin ficewar Isra’ila.”
Trump ya yi barazanar cewa Isra’ila za ta samu cikakkiar dama domin ruguza Hamas idan kasashen Larabawa da na Musulunci suka gaza magance wannan batu. Ya kuma yi gargadin cewa Netanyahu zai samu cikakken goyon baya don yin duk abin da ya ga dama idan Hamas ba ta amince da shawararsa ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump: Za mu goyi bayan Netanyahu idan Hamas ba ta amince da kudirinmu ba September 30, 2025 Iran: An zartar da hukuncin kisa a kan wani babba dan leken asirin Isra’ila September 30, 2025 Axios: Netanyahu ya nemi afuwar Qatar kan harin da Isra’ila ta kai a kan Doha September 30, 2025 Larijani: Iran a shirye take don tallafawa Lebanon da gwagwarmaya a kowane mataki September 30, 2025 Takunkumin makamai na Turai ya haifar da mummunar illa ga tattalin arzikin sojojin Isra’ila September 30, 2025 Kungiyar Yan Gudun Hijira Na Kasar Noway Tace Akwai Babbar Damuwa Game Shiru Kan Gaza September 29, 2025 Shugaban Iran: Yunkurin Durkusar Da Alummar Iran Bashi Da Maraba Da Mafarki. September 29, 2025 Kwamitin Tsaro A Majalisar Dokokin Iran Ta Gama Tsara Ficewar Kasar Daga NPT September 29, 2025 An Kashe Sojan HKI Guda A Harin Maida Martani A Yankin Yamma Da Kogin Jordan September 29, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Cewa Bukatun Amurka Daga Iran Ba Mai Yuwa Ba Ne September 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Amince Da Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin
Kasar Benin ta amince da sabon tsarin Mulki da ya amince da sabbin sauye-sauye a tsarin Mulki wanda ya kunshi kafa majalisar dattijai da kuma tsawaita wa’adin shugabancin kasa da na ‘yan majalisu.
Sabon wa’adin da ‘yan majalisar dokokin kasar su ka amince da shi, shi ne shekaru bakwai, bayan da ya kasance shekaru biyar. Sai a shekara mai zuwa ta 2026 ne dai sabbin sauye-sauyen da aka yi za su fara aiki.
Sai dai shugaban kasar da yake ci a yanzu Patrice Talon ba zai ci moriyar wannan sauyin ba saboda watanni bakwai su ka rage masa wa’adinsa na biyu yak are.
A karkashin sauye-sauyen da aka yi, an kirkiro majalisar dattijai da za ta kasance da mambobi 25 zuwa 30. Kuma wadanda za a zaba su zama wakilai a wannan majalisar ta dattijai su ne masu kwarewa a fagen siyasa, tsaro, tsofaffin shugabannin kasashe, tsoffin ‘yan majalisar dokoki, alkalai da kuma jami’an soja.
Daga cikin aikin da majalisar dattijan za ta yi da akwai karfafa hadin kan kasa, demokradiyya da zaman lafiya. Har ila yau Majalisar za ta rika yin bita ta biyu ta duk wata doka da majalisar dokoki za ta amince da ita,musamman wadanda su ka shafi harkokin kudi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon November 16, 2025 Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya November 16, 2025 Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran November 16, 2025 Kanada Ta Tsare Tsohon Wakilin Majalisar Dinkin Duniya Mai Bincike Kan Laifukan Yakin Israila. November 16, 2025 Zarfi: HKI Ce Kawai Take Ayyana Nukiliya Ba Bisa Kaida Ba A Yammacin Asiya. November 16, 2025 Shugaban kasar venuzuwela Yayi Tir Da Atisayan Soji Da Trinidad and Tobago Ke yi. November 16, 2025 IRGC ta kama wani jirgin ruwan dakon mai a gabar tekun kudancin Makran November 16, 2025 Iran : sojojin Amurka a yankin Caribbean barazana ne ga zaman lafiya November 16, 2025 Lebanon za ta kai karar Isra’ila a MDD kan gina Katanga a iyakarta November 16, 2025 AU ta sake watsi da ikirarin Trump cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya November 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci