Aminiya:
2025-11-18@12:33:43 GMT

’Yan sanda sun kama kwayoyin N165.4m da makamai a Kano

Published: 29th, September 2025 GMT

’Yan sanda sun kama miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 165.4 a watan nan na Satumba a Jihar Kano.

Daga ciki, jami’an rundunar sun kama kwayoyin da kudinsu ya kai Naira miliyan 82.7 a unguwar Rimin Auzinawa, suka mika ga Hukumar Yaki da Ta’ammali da Miyagun Kwayoyi (NDLEA) domin kammala bincike da gurfanarwa a gaban kuliya.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa rundumar ta kuma kama kwayoyin Tramadol da kudinta ya kai Naira miliyan 60.3 da kwayar Pregabalin ta Naira miliyan 22.4 da kuma sinki 523 na tabar wiwi da injinan tura kudi na POS guda biyar daga hannun wadanda ake zargi a sassan jihar.

Kwamishinan ya ci gaba da cewa rundunar ta kama mutum 105 da ake zargi da safara miyagun kwayoyin da mallakar miyagun makamai da sauran laifuka.

An sallami Kwamishinar Mata ta Jihar Bauchi daga aiki Ranar Laraba jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai dawo aiki 

Daga cikin mutanen, ana zargin 17 da laifin fashi da makami, 8 da zargin dillacin kwayoyi da kuma 9 zargin satar motoic, masu satar babur biyar da ’yan daba 57 da kuma barayi 9.

Ya ce kayan laifin sun hada da bindigogi kirar Ak-47 guda uku, Pistol guda 6, AK-47, da sauran bindigogi kirar gida guda uku, harbi-ruga guda daya da albarusai da takubba da adduna da wukake da Dan-Bida. Sauran sun hada da motoci biyu, A Daidaita Sahu biyu, babura 13 da shanu uku da wasu kayan sata iri-iri.

Ya danganta nasarar da umarbin Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, na hadin gwiwa da al’umma wajen dakile ayyukan laifi gabanin bukukuwan.

Ya bayyana cewa sashen Operation Kukan Kura da rundunar ta kafa ya taka muhimmiyar rawa wajen takaita ayyukan laifi ta hanyar hadin kan al’ummar gari.

Kwamishinan ya yaba wa al’ummar jihar bisa irin hadin kai da suke ba wa rundunar, wanda ya ce ya taimaka matuka wajen dakile barazanar tsaro daga bata-gari.

Ya kara da kiran su da su ci gaba da taimaka wa rundunar da muhimman bayanai da za su taimaka wajen dorewar nasarar da aka samu kan masu aikata miyagun laifukan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan sanad kwayoyi Miyagun Kwayoyi Tabar wiwi zarg Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Rundunar Ƴansandan birnin tarayya ta bayyana cewa babu wani rahoto ko bayanin da ta samu game da yunkurin kashe laftanar Ahmed Yerima, jami’in Sojin ruwa da ya yi taƙaddama da Ministan Abuja, Nyesom Wike, kan wani fili da ake jayayya kansa a Abuja kwanakin baya. Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar, SP Josephine Adeh, ta fitar da sanarwar ne a ranar Litinin tana mai ƙaryata labarin da ya yaɗu a kafafen sada zumunta.

Adeh ta ce babu wani lamari da ya faru ko aka rubuta a koda ɗaya daga cikin wata ƙaramar hukumar da ke cikin birnin, don haka ta buƙaci jama’a da su yi watsi da labarin saboda ba shi da tushe. Ta ƙara da cewa irin waɗannan labaran karya na iya tayar da hankalin jama’a da haddasa tashin hankali ba tare da dalili ba.

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

Rundunar ta kuma shawarci jama’a da su yi taka-tsantsan wajen yaɗa bayanan da ba su tabbata ba, tare da samar da sahihan hanyoyin samun bayanai idan wani abu ya taso. Ta ce kare lafiyar jama’a da tabbatar da zaman lafiya shi ne babban aikin da rundunar ta sa a gaba.

ADVERTISEMENT

A ƙarshe, rundunar ta buƙaci mazauna Abuja da su riƙa kai rahoton duk wani abin da suka ga ya saɓa wa tsaro ga ofishin ƴansanda mafi kusa, ko kuma su tuntuɓi shalƙwatar rundunar ta hanyar layukan gaggawa: 08032003913 da 08068587311 domin samun kulawa cikin gaggawa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon November 17, 2025 Manyan Labarai Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja November 16, 2025 Manyan Labarai Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su November 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno
  • ’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a Gombe
  • ’Yan sanda sun kama ƙunshe 66 na Tabar Wiwi a Gombe
  • Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda
  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato
  • Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso
  • Sanusi ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — Kwankwaso
  • Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94