Leadership News Hausa:
2025-10-19@07:35:04 GMT

Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno

Published: 13th, April 2025 GMT

Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno

Wasu karin majiyoyi sun nuna cewa, wannan hanyar ta hada Maiduguri da wasu kananan hukumomi da ke kudancin jihar Borno, wacce ta kasance yankin da yan ta’addan Boko Haram ke yawan kai hare-hare tsawon shekaru.

 

A baya hanyar, ta kasance a rufe amma Gwamnan jihar, Farfesa Babagana Zulum ya bude ta, domin bai wa jama’a damar ci gaba da zirga-zirga a yankin da suka hada da Damboa, Chibok da sauran kananan hukumomi a kudancin Borno tare da taimakon rakiyar sojoji a matsayin kariya.

 

An kwashe wadanda suka rasun tare da wadanda suka jikkata, wanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba, zuwa asibiti a Maiduguri domin samun kulawar likitoci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun tallafa wa mutanen Yobe da N23m bayan harin kuskure

Rundunar Sojin Saman Najeriya, ta bai wa mutanen garin Buhari da ke Karamar Hukumar Yunusari a Jihar Yobe, tallafin Naira miliyan 23 tare da alƙawarin gina rijiyar ruwa mai amfani da hasken rana.

Wannan tallafi ya biyo bayan wani harin kuskure da jiragen yaƙin rundunar suka kai a watan Satumba 2021, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane takwas da jikkata wasu 30.

Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban Jam’iyyar APC HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya

Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritay), wanda shi ne mai bai wa Gwamna Buni shawara kan harkokin tsaro, ya bayyana cewa wannan tallafi ya nuna tausayin gwamnati da rundunar sojan sama ga al’ummar garin.

Ya ce, tun bayan faruwar lamarin, gwamnan Yobe Mai Mala Buni da Gwamnatin Tarayya suna ƙoƙari wajen taimaka wa waɗanda abin ya shafa.

A madadin Babban Hafsan Sojin Sama, Komando U.U. Idris na rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), ya ce rundunar ta bayar da Naira miliyan 23 ga iyalan waɗanda suka rasu da kuma naira dubu 500 ga kowane mutum daga cikin waɗanda suka jikkata.

Ya ƙara da cewa, rundunar ta yi wa wadanda suka rasu addu’a, tare da fatan Allah Ya kiyaye faruwar irin hakan a nan gaba.

A nasa jawabin, Alhaji Ali Lawan, wanda ya wakilci al’ummar garin Buhari, ya gode wa rundunar Sojin Sama bisa wannan taimako.

Ya kuma roƙi jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen yaƙar ’yan ta’adda, domin har yanzu yankin na fuskantar barazanar tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun tallafa wa mutanen Yobe da N23m bayan harin kuskure
  • HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya
  • NSCDC Ta Kama Wadanda Ake Zargi Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Kaduna
  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara
  • Kungiyar Euro-Med ta bukaci bangarori su shiga Gaza domin tattara bayanai kan kisan kiyashin Isra’ila
  • Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC
  • Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina