Leadership News Hausa:
2025-11-14@20:33:09 GMT

Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno

Published: 13th, April 2025 GMT

Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno

Wasu karin majiyoyi sun nuna cewa, wannan hanyar ta hada Maiduguri da wasu kananan hukumomi da ke kudancin jihar Borno, wacce ta kasance yankin da yan ta’addan Boko Haram ke yawan kai hare-hare tsawon shekaru.

 

A baya hanyar, ta kasance a rufe amma Gwamnan jihar, Farfesa Babagana Zulum ya bude ta, domin bai wa jama’a damar ci gaba da zirga-zirga a yankin da suka hada da Damboa, Chibok da sauran kananan hukumomi a kudancin Borno tare da taimakon rakiyar sojoji a matsayin kariya.

 

An kwashe wadanda suka rasun tare da wadanda suka jikkata, wanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba, zuwa asibiti a Maiduguri domin samun kulawar likitoci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Gidauniya Ta Kaddamar Da Kwamiti Kan Mata A Nasarawa

Gidauniyar  fadakar da al’umma akan dokoki da ka’idoji ta Nijeriya ta kaddamar da kwamiti a jihar Nasarawa domin aiwatarwa da sa ido kan shirin mata, zaman lafiya da tsaro, da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa wajen gina zaman lafiya a cikin jihar.

Daraktan gudanarwa na gidauniyar, Mista Peter Maduoma, ne ya bayyana hakan a Lafia yayin taron horarwa na kwanaki uku da aka shirya ga masu ruwa da tsaki kan batun mata, zaman lafiya da tsaro, wanda gidauniyar ta shirya.

Mista Maduoma, wanda Jami’in Shari’a da Albarkatun Ƙasa na Gidauniyar, Mista Ifeyinwa Akwiwu, ya wakilta, ya ce shirin wani ɓangare ne na aikin gidauniyar mai taken “Ƙarfafa tsarin adalci ta hanyar kare haƙƙin ɗan adam da bunƙasa zaman lafiya a Najeriya.”

Ya bayyana cewa ana aiwatar da wannan shiri ne a jihohi biyar — wato Benue, Nasarawa, Plateau, Kaduna da Imo, domin haɓaka ingantaccen tsarin haɗin kai da amfani da bayanai wajen magance rikice-rikice ta hanyar tsarin da ya dace da bukatun mata.

Ya ƙara da cewa gidauniyar, tsawon shekaru 27, tana aiki wajen inganta tsaron jama’a, zaman lafiya da adalci a Najeriya da ma nahiyar Afrika ta hanyar bincike da fadarwa akan dokoki, da haɗin gwiwa da gwamnati da ƙungiyoyin farar hula.

A nasa jawabin, Kwamishinan Shari’a kuma Babban Lauyan Jihar Nasarawa, Barista Isaac Danladi, ya yaba da muhimmiyar rawar da mata ke takawa a al’umma, yana mai cewa ma’aikatarsa ta tanadi matakai na tabbatar da gurfanar da masu aikata ta’addancin fyade da cin zarafi ga mata, domin zama izina ga wasu.

Ita ma Kwamishinar Mata da Harkokin Jin Kai ta Jihar Nasarawa, Hajiya Hauwa Jugbo, ta bayyana shirinta na yin haɗin gwiwa da duk ƙungiyoyin da ke da sha’awar kare haƙƙin mata, tare da bada tabbacin cewa ma’aikatarta za ta goyi bayan cikakken aiwatar da dokoki da ke tabbatar da haƙƙin mata da adalci ga waɗanda aka zalunta.

Aliyu Muraki, Lafia.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Wata Gidauniya Ta Kaddamar Da Kwamiti Kan Mata A Nasarawa
  • MDD ta yi gargadi game da hadarin yunwa a wasu sassa na duniya
  • Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
  • ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa
  • Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna