Aminiya:
2025-11-19@14:20:55 GMT

Dukiyar sama da miliyan 500 ta kone a gobarar kasuwar katako ta Gombe

Published: 19th, November 2025 GMT

Shugaban ƙungiyar masu sayar da tsofaffin ƙarafa a jihar Gombe, A.A. Laja, ya ce gobarar da ta tashi a kasuwar tsofaffin ƙarafa da ke kasuwar katakon jihar ta jawo masa asara da ta kai sama da Naira miliyan 500.

Lamarin ya faru ne a daren Laraba, inda wutar ta ƙone shaguna fiye da 30 da ke ɗauke da kayan kasuwancinsa.

Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’

A.A Laja, wanda ya yi magana da wakilinmu jim kaɗan bayan aukuwar lamarin, ya ce gobarar ta tashi ne da misalin karfe 10 na dare, ta kuma ci gaba da ci har zuwa karfe 4:00 na Asuba, saboda rashin isowar jami’an kashe gobara cikin lokaci.

“Mun kira tashar kashe gobara ta Dukku da ta Bauchi, amma duk suka ce basu da ruwa. Na tafi har Jami’ar Jihar Gombe, amma sai da shugaban Karamar Hukumar Gombe Barista Sani Ahmad Haruna, ya yi musu waya kafin su turo mota. Wuta ta ci rabonta sosai kafin su iso,” in ji shi.

Ya ce shi kaɗai ne gobarar ta shafa saboda dukkan shagunan nasa ne, kuma dukkan kayan cikinsu nasa ne.

A cewar dan kasuwar kayan da wutar ta cinye sun hada da kayan gine-gine, katako, tsofaffin injuna, da sauran kayayyaki masu tsada da ya samo daga cikin gida da ƙasashen waje.

“Kayan aikin gini kaɗai da ke wajen sun yi yawa sosai. Ina da ma’aikata sama da 100, wannan abu ya shafe mu matuƙa,” in ji shi.

Ya yi alla-wadai da abin da ya kira sakacin jami’an kashe gobara, yana mai cewa da sun zo da wuri da asarar ba ta kai haka ba.

Sai dai ya jinjina wa shugaban Karamar Hukumar Gombe saboda matakin gaggawa da ya ɗauka.

Da wakilinmu ya tuntubi shugaban Karamar Hukumar Gombe, wanda kuma shi ne shugaban ALGON a jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, ya tabbatar da ziyartar wurin a lokacin da gobara ke ci.

Ya ce, “Na ziyarci kasuwar tsofaffin Karafa da ke kasuwar katako lokacin da gobarar take ci. Asarar ta yi yawa, amma har yanzu ba za mu iya fitar da cikakken adadi ba. Muna jajanta wa wanda lamarin ya shafa,” inji shi.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da tallafawa jama’a a irin waɗannan lokuta, tare da godiya ga mazauna unguwar da suka taimaka wajen kare kadarorin mutane daga masu sace-sace a lokacin gobarar

Sai dai duk yunkurin jin ta bakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Gombe da wakilinmu ya yi ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan labarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobarar Gombe

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16

Gwamnatin Jihar Gombe ta raba sabbin motoci ƙirar SUV guda 16 ga Alƙalai na Babbar Kotu da Khadi-Khadi na Kotun Shari’a domin taimaka musu wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata a fadin jihar.

Motocin sun haɗa da motoci biyu ƙirar Toyota SUV samfurin 2025 da aka bai wa babban alƙal8 da Grand Khadi.

Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa

Motocin guda 14 ƙirar GAC SUV samfurin 2025 da aka raba wa sauran alƙalai da khadi-khadi.

Da yake miƙa motocin, Mataimakin Gwamna Mannasah Daniel Jatau, ya ce gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na ƙoƙari wajen samar da kayan aiki na zamani domin inganta ayyukan gwamnati, musamman a ɓangaren shari’a.

Ya ce gwamnati na magance matsalolin da ta gada, ciki har da biyan fansho da biyan albashi a kan lokaci.

Ya kuma yi kira ga waɗanda aka bai wa motocin da su yi amfani da su wajen gudanar da ayyukansu.

A nasa jawabin, Kwamishinan Kuɗi, Muhammad Gambo Magaji, ya bayyana cewa an kashe sama da Naira biliyan biyu wajen sayen motocin.

Ya ce tsawon sama da shekaru 10 ɓangaren shari’a bai samu sabbin motocin aiki ba.

Kwamishinan Shari’a, Barista Zubair Muhammad Umar, ya ce rabon motocin wani ɓangare ne na cika alƙawarin gwamnati na inganta ɓangaren shari’a.

Ya tunatar da cewa aikin gina sabon ginin Babbar Kotu na kimanin Naira biliyan 16 na ci gaba da gudana.

A jawabinsa na godiya, Babban Magatakardar Babbar Kotu, Barista Bello Shariff, ya yaba wa gwamnatin jihar bisa goyon bayan da ta ke bai wa bangaren shari’a.

Ya bayyana cewa za su yi amfani da motocin ta hanya mai kyau domin inganta ayyukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’
  • Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe
  • Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • ’Yan sanda sun kama ƙunshi 66 na Tabar Wiwi a Gombe
  • ’Yan sanda sun kama ƙunshe 66 na Tabar Wiwi a Gombe
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16