Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa
Published: 20th, November 2025 GMT
Shugaban majalisar dokokin kasar Labanon Nabih Berri yayi kira da a gudanar da taron gaggawa na kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya domin tattaunawa kan ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da Israi’la ke yi kan kasar Labanon, wanda ya kashe mutane 14 , kuma ya jaddada game da muhimmancin shigar da kara a hukumance ga majalisar dinkin duniya.
Wannan bukata ta zo ne adaidai lokacin da sojojin Isra’ila suke kai hare hare kan fararen hula dake jawo asarar rayuka, kuma yake jawo fargaba game da ci gaba da hara-haren israila na keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta mai lamba 1701, Isra’ila ta kai hare hare a lokuta daban daban a kudancin labanon kuma yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama.
Nabih Birri ya kara da cewa Isra’ila taci gaba da kai hare hare kan fararen hula, yara da kuma dalibai wanda na baya bayan ne shi ne ta kai a garin Al- Tira,
Ana ta bangaren kungiyar hizbullah ta yi tir da harin kisan kare dangi da sojojin Isra’ila ke yi a kudancin labanon ,kuma ta bayyana shi a matsayin mummunan aiki dake kara yawan tarihin laifukan yaki kan alummar falasdinu da ma labanon dama sauran mutanen yankin da Isra’ila ke yi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Achraf Hakimi Ya Zama Gwarzon Wasan Kwallon Kafar Afirka Na Shekara Ta 2025 November 20, 2025 Kasashen Iran Da Malesiya Sun Rattaba Hannu Kan Jarjejeniyar Fadada Dangantakar Addini November 20, 2025 Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam November 20, 2025 Iran : daftarin kudurin da Canada ta gabatar, siyasa ce da kin jininmu November 20, 2025 AU ta yi Allah-wadai da tsoma bakin kasashen waje a harkokin tsaron Afirka November 20, 2025 Amurka ta Shawarci Ukraine ta amince da yankunan da Rasha ta mamaye mata November 20, 2025 Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar November 20, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka November 19, 2025 Sojojin Yemen Suna Da Makami Mai Linzami Da Babu Mai Makamancinsa Sai Iran November 19, 2025 Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar November 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing
A yau ne aka bude taron tattaunawa game da wayewar kai takanin Sin da kasashen Larabawa karo na 11, wanda sashen cudanya da kasashen waje na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin da sakatariyar kawancen kasashen Larabawa suka dauki nauyin shiryawa a Beijing.
A gun taron, shugabanni na jam’iyyu da kungiyoyin siyasa, ‘yan majalisa, jami’an gwamnati, da wakilan masana da kafofin watsa labarai daga Sin da kasashen Larabawa guda 22 sun hallara don inganta ilmantarwa da fahimtar juna kan wayewar kai da kuma zurfafa hadin gwiwar abokantaka.
A wannan taron kuma, Sin da kasashen Larabawa za su mayar da hankali kan batutuwa kamar “Musayar darussan mulkin kasa da binciken hanyoyin zamanantarwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa”, da “Shawarwarin wayewar kan duniya da hadin gwiwar al’adu na Sin da kasashen Larabawa”, da kuma “Shawarar ziri daya da hanya daya da hadin kan jama’a tsakanin Sin da kasashen Larabawa”, kana za su shiga tattaunawa da musayar ra’ayoyi masu zurfi.(Safiyah Ma)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA