Sanarwar ta ƙara da cewa, ƙungiyar ta karrama gwamna Lawal tare da gwamnonin Akwa Ibom, Kaduna, da kuma jihar Legas.

 

“A jiya a Legas, ƙungiyar ‘yan kasuwa ta Nijeriya da Amurka (NACC) ta gudanar da bikin cika shekaru 65 da ƙaddamar da Alhaji Sheriff Balogun a matsayin shugaban ƙungiyar na 20.

 

“Taron mai taken ‘Ƙarfin Haɗin Kai: Shekaru 65 na inganta dangantakar tattalin arzikin Nijeriya da Amurka’ ya samu halartar manyan jami’an Amurka da Nijeriya da kuma ‘yan kasuwa.

 

“Ƙungiyar ta amince da goyon bayan da Gwamna Lawal yake baiwa harkokin kasuwanci a jihar Zamfara, musamman a fannin noma.

 

“Karramawar da aka baiwa gwamnan na nuni ne da irin kwazonsa na jagoranci, da kwazonsa na inganta ilimi, da kuma jajircewarsa wajen magance matsalar rashin tsaro.

 

“Ƙungiyar ta kuma yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa inganta rayuwar al’ummar Zamfara ta hanyar ba da fifiko wajen samar da kiwon lafiya, ilimi, noma, da kuma ayyukan ƙarfafawa guiwar al’umma.”

 

Yayin karbar lambar yabon, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirinsa na inganta rayuwar al’ummar Jihar Zamfara ta hanyar inganta ayyukan yi.

 

“Ina so in gode wa shugabannin ƙungiyar ‘yan kasuwa ta Nijeriya da Amurka da suka ga na cancanci wannan karramawa, hakan zai ƙara min kwarin guiwa na ƙara himma, wannan na ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara ne.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya da

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Ƙwato Bindigogi Da Tabar Wiwi A Zamfara Bayan Artabu Da ‘Yan Bindiga

Kwamishina CP Ibrahim Maikaba ya yaba da ƙoƙarin jami’ansa, yana kuma ƙara jaddada niyyar rundunar na yin aiki tare da al’umma domin samar da tsaro.

Ya buƙaci mutane su riƙa bai wa rundunar sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa yaƙi da laifuka.

Rundunar ta kuma fitar da lambobin da za a iya kira idan aka ga wani abu da ba a gamsu da shi ba; 08034805544, 07032490813 da kuma 09053872244

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Fira Ministan Indiya Ya Bayyana Cewa: Iran Tana Kokari A Fagen Inganta Zaman Lafiya A Yanki Da Duniya Baki Daya
  • Amurka Ta Ce: Shugaban Rikon Kwarayar Siriya Al-Julani Ya Yi Alkawarin Cewa Ba Zai Cutar Da Tsaron Isra’ila Ba
  • Hakimin Kafin Hausa Ya Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyuka Cigaban Al’umma
  • Sarkin Daura Zai Karrama Ja’o’ji Da Wasu Samarin Arewa
  • Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
  • Gwamna Buni Ba Zai Shiga Hadakar Jam’iyyun Adawa ba – Mai Magana Da Yawunsa
  • Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’
  • ‘Yansanda Sun Ƙwato Bindigogi Da Tabar Wiwi A Zamfara Bayan Artabu Da ‘Yan Bindiga