Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya
Published: 19th, November 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta shiga cikin jimami a ranar Laraba bayan mutuwar Sanata Okey Ezea, mai wakiltar mazabar Enugu ta Arewa.
Bayanai sun nuna marigayin ya rasu ne a kasar Burtaniya inda yake jinya.
‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’ Mai taɓin hankali ya kashe soja a LegasEzea, wanda aka zaɓe a ƙarƙashin jam’iyyar LP, shi ne kaɗai Sanatan da ya ci zabe daga Enugu karkashin jam’iyyar a Majalisar Dattawa ta 10.
Rasuwarsa ta sa ya zama sanata na biyu daga yankin Kudu maso Gabas da ya rasu cikin shekaru biyu, bayan mutuwar Sanata Ifeanyi Ubah daga Jihar Anambra, wanda shi ma ya rasu a Landan a watan Yuli 2024 yana da shekara 52.
Da labarin rasuwarsa ya isa Majalisar, abokan aikinsa sun yi ta’aziyya, suna bayyana shi a matsayin ɗan majalisa mai tawali’u, mai jajircewa, da kuma sadaukarwa, wanda rashin sa ya bar gibi a zauren majalisar.
Sanata Orji Uzor Kalu, wanda ke wakiltar Abia ta Arewa, ya ce ya yi matukar kaduwa da samun labarin, inda ya bayyana marigayin a matsayin ɗan’uwana kuma abokinsa.
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan daga Kogi ta Tsakiya, ita ma ta yi jimami, tana bayyana Ezea a matsayin aboki mai hikima da natsuwa, wanda shawarwarinsa da addu’oinsa suka taimaka mata a lokutan da ta shiga ƙalubale.
Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta yi magana a hukumance kan rasuwarsa a zaman majalisa, tare da yin shiru na minti ɗaya don girmamawa, kamar yadda al’ada ta tanada.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
PDP Ba Ta Mutu Ba Duk Da Rikicin Da Ta Ke Fama Da Shi – Anyanwu
“Lokacin da Wike, Makinde, Ugwuanyi, Ikpeazu da Ortom suka kafa G5, bana are da su. Amma duk da haka, Wike abokina ne sosai. Lokacin da PDP ta samu matsala Wike ne ya yi ƙoƙarin tallafa mata,” in ji Anyanwu.
Ya ƙara da cewa Wike bai fice daga PDP ba.
Anyanwu ya kira taron gangamin PDP da aka yi a Ibadan a matsayin ɓata lokaci, yana mai cewa ba a yi sa bisa ƙa’ida ba.
Ya ce dakatar da shi daga matsayin Sakataren jam’iyyar na Ƙasa ba a kan ka’ida yake ba saboda jam’iyyar ba ta bi umarnin kotu ba.
Ya kuma ce taron bai haɗa jihohi da dama ba, don haka bai samu cikakken goyon baya ba.
A yayin babban taron na PDP na 2025, jam’iyyar ta kori Wike, tsohon gwamnan Ekiti Ayodele Fayose, Samuel Anyanwu da wasu, bisa zargin cin amanar jam’iyyar.
Haka kuma ta rushe shugabancin jam’iyyar a Imo, Abia, Enugu, Akwa Ibom da Ribas.
Bode George, wani jigo a jam’iyyar PDP ne, ya gabatar da ƙudirin korar manyan mambobin 11, kan zarginsu da gudanar da abubuwan suka saɓa wa dok6 jam’iyya.
Shugaban PDP na Jihar Bauchi ya mara masa baya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA