Aminiya:
2025-11-19@08:41:17 GMT

Mai taɓin hankali ya kashe soja a Legas

Published: 19th, November 2025 GMT

Wani mutum da ake zargin yana fama da matsalar tabin hankali ya kai hari tare da kashe wani soja a yankin Imota da ke Ikorodu a jihar Legas.

Lamarin, wanda ya faru a fili da rana tsaka a ranar Lahadi, ya sa makwabtan wurin da dama guduwa don neman tsira.

Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis

Shaidu sun bayyana cewa wanda ya kai harin, wanda ba shi da makami sai sanda ta itace, ya kusanci sojan ya dinga dukan shi da sandar.

Sojan da ya rasu, wanda aka ce yana aiki a karkashin Operation AWASE, rundunar haɗin gwiwa ta musamman da ke yaki da laifuka a jihar, ya mutu sakamakon raunukan da ya samu.

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, 16 ga Nuwamba, 2025, da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, lokacin da aka tura sojan don aikin tsaro na cikin gida.

Rundunar Sojojin Najeriya ta 81 ta tabbatar da faruwar lamarin, tare da yin ta’aziyya ga iyalan sojan da ya rasu.

Mai rikon mukamin Daraktan Hulɗa da Jama’a na shiyyar, Musa Yahaya, ya bayyana a ranar Talata cewa sojan yana ƙoƙarin kwantar da tarzoma ne lokacin da mai harin ya bugi kansa da sanda mai nauyi, wanda ya jawo masa mummunan rauni.

Ya kuma ce sauran sojoji sun hanzarta shawo kan lamarin, suka kashe mutumin tare da dawo da makamin sojan.

Yahaya ya ƙara da cewa an garzaya da sojan da ya ji rauni zuwa Asibitin Gwamnati da ke Ikorodu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Ya ce tuni aka fara gudanar da bincike kan lamarin, kuma rundunar sojoji ta yi kira ga jama’a da su kasance masu lura da kuma bayar da rahoton duk wani abun da ba su yarda da shi ba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara

’Yan bindiga sun kashe mutum 3 tare da yin garkuwa da wasu 64 a ranar Asabar a Karamar Hukumar Tsafe ya Jihar Zamfara.

Cikin waɗanda ’yan ta’addan suka kashe har da wani jigon jam’iyyar APC, Hon. Umaru Moriki wanda aka bindige a kan hanyar Gusau zuwa Tsafe, waɗanda aka yi garkuwa da su kuma har da mata da ƙananan yara a kauyen Fegin Baza.

Harin ta faru ne washegarin da Ministan Tsaro, Bello Matawalle ya ziyarci jihar, inda ya sanar cewa Hedikwata Tsaro ta girke ƙarin jami’an tsaro a jihar.

A yayin ziyarar ministan ya bayyana cewa zai gana da jami’an tsaro inda zai ba su umarni kar su raha wa ’yan ta’adda.

NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi

Ministan ya kuma zargi gwamnatin jihar kan abin da yake yi da kuɗaɗen da take samu daga Gwamnatin Tarayya.

Jihar, wadda ita ce mahaifar Matawalle, tana fama da matsalar hare-haren ’yan bindiga da suka hana ayyukan noma da sauran harkokin tattalin arziki.

Hare-haren bayan nan, kari ne a kan wasu da dama da suka addabi jihar, duk da ayyukan soji da dama domin daƙile matsalar.

Yadda abin ya faru

Rahotanni sun ce ’yan bindiga kusan 30 ne suka buɗe wuta kan motar Hon. Moriki yayin da yake kan hanyarsa zuwa Kaduna, inda suka kashe shi nan take.

Bayan haka, sun yi garkuwa da mazauna kauyen 64, suka tafi da su zuwa wani wurin da ba a sani ba.

Hon. Moriki, wanda ya taɓa tsayawa takarar kujerar Majalisar wakilai a Mazaɓar Zurmi/Shinkafi, shi ne Sarkin Fada na Moriki a halin yanzu.

Ɗan marigayin, Abubakar Umar Moriki, ɗalibi a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “Baba ya yi ƙoƙarin yin u-turn bayan ya lura da ’yan bindiga, amma suka buɗe masa wuta. An harbe shi, ya rasu nan take. An yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci. Allah Ya gafarta masa, ya kuma sanya shi da Aljanna Firdaus.”

An gudanar da sallar jana’izar marigayi a Masallacin Juma’a na Federal Low-cost, Tudun Wada da ke Gusau, ƙarƙashin jagorancin Imam Alƙali Abdullahi Yakubu.

Ministan Tsaron Ƙasa, Alhaji Bello Mohammed Matawalle, ya halarci jana’izar tare da yin ta’aziyya ga iyalan marigayin.

Matawalle ya bayyana rasuwar Hon. Moriki a matsayin babban rashi ga jihar da ƙasa baki ɗaya, la’akari da ayyukan alheri da ya yi wa jama’a, musamman maƙwabta da ’yan uwa.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun APC na jihar, Yusuf Idris, ya fitar, Matawalle ya yi addu’ar Allah Ya saka masa da Aljanna Firdaus, ya kuma ba iyalansa ƙarfin zuciya wajen jure wannan rashi.

Ministan ya bayar da gudummawar Naira miliyan 10, buhunan shinkafa 50, buhunan masara 25 da buhunan gero 25 ga iyalan marigayin, tare da tabbatar musu da kulawa daga gwamnati.

A madadin iyalan marigayin, Ambassador Abubakar Hussaini Moriki ya gode wa ministan bisa kulawa da tausayi da ya nuna.

Ya ce sun san cewa ministan ya soke dukkan ayyukansa na yau domin halartar jana’izar, ya kuma yi tafiya daga garin Maradun zuwa Gusau don yin ta’aziyya da su a wannan lokaci na jarrabawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
  • Iran: An Bayyana Taron Gundumomin Dake Gabar Ruwan ” Caspian” Da Cewa Yana Bunaksa Alakar Kasashen Yankin
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi
  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
  • ’Yan Bindiga A Kano: Sanusi II ya ziyarci Faruruwa, ya buƙaci a tsaurara tsaro
  • Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba
  • Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya