Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano
Published: 20th, November 2025 GMT
Wani magidanci tare da ɗaukacin iyalinsa huɗu sun rasu sakamakon wata gobara da ta tashi a sanadin kunna maganin sauro a layin Baba Impossible da ke Unguwar Kundila, da ke Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano.
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da tashin wutar da misalin ƙarfe 4:13 na Asubar ranar Laraba.
Mai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce sun samu kiran wani ma’aikacinsu, HFS Abba Datti, game da gobarar.
A cewarsa ba tare da ɓata lokaci ba suka tura jami’ansu daga hedikwatar hukumar zuwa wajen da gobarar ta tashi.
“Lokacin da muka isa, mun ga wani gida mai girman ƙafa 40 da 30 yana ƙone gaba ɗaya. Gobarar ta shafi ɗakuna biyu, falo, bayan gida, da kuma ɗakin girki,” in ji sanarwar.
Mutane biyar ne gobarar ta rutsa da su; mai gidan mai suna Shodandi mai shekara 43, matarsa Rafi’a mai shekara 30.
Ragowar kuma ’ya’yansu ne; Mardiya Shodandi mai shekara uku, Yusira Shodandi ’yar shekara ɗaya da rabi da Aminu Shodandi ɗan watanni 12.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Huɗu daga cikinsu; uba, uwa, da ƙananan yara biyu sun ƙone kafin a ceto su. Amma an samu damar ceto Aminu ɗan watanni 12.”
Hukumar ta miƙa saƙon ta’aziyyarta ga iyalan mamatan, ta kuma ta gargaɗi mutane da suke kula sosai, musamman a lokacin sanyi.
Bincike ya nuna cewa gobarar ta samo asali ne daga maganin sauro da matatan suka kunna a falo, sannan suka yi barci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara iyali rasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
CAF ta fitar da ’yan wasa uku da suka rage a takarar gwarzon Afirka na bana
Hukumar ƙwallon ƙafar Afirka CAF, ta bayyana cewa bayan tankade da rairaya da ta yi, a yanzu ’yan wasa uku kacal ne suka rage a takarar gwarzon nahiyyar na bana.
A wata sanarwar da hukumar ta fitar a ranar Lahadi, ta bayyana Achraf Hakimi da Mohamed Salah da Victor Osimhen, a matsayin sauran ukun da suka rage a takarar gwarzon dan ƙwallon ƙafar Afirka na bana.
Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a BornoHakimi, kyaftin din Morocco, ya lashe kofuna daga ciki har da Champions League a PSG — na farko a tarihin ƙungiyar — da Ligue 1, da European Super Cup, da kuma kai wa zagayen ƙarshe a FIFA Club World Cup da Chelsea ta lashe a Amurka.
Shi kuwa Mohammed Salah ya taka rawar gani a Liverpool a kakar da ta wuce da lashe Premier League, kuma shi ne kan gaba a zazzaga kwallaye mai 29 da bayar da 18 aka zura a raga, hakan ya sa ya karbi kyautar takalmin zinare, wato Golden Boot.
Mohammed Salah dan ƙasar Masar mai shekara 33 na fatan karbar kyautar gwarzon Afirka karo na uku bayan 2017 da kuma 2018.
Shi kuwa dan ƙwallon tawagar Super Eagles ta Najeriya, Victor Osimhen ya jagoranci Galatasaray ta dauki babban kofin tamaula na Turkiya da cin ƙwallo 26.
Osimhen ya taba zama gwarzon Afirka 2023 a lokacin da shi kuma Hakimi ya yi na biyu
To sai dai mai riƙe da kyautar a yanzu, wato Ademola Lookman na Nijeriya, bai kai bante ba a kakar nan sakamakon gaza taka rawar gani yadda ake buƙata.
Za a gudanar da bikin karrama gwarzon dan ƙwallon ƙafa na Afirka na bana ranar Laraba a birnin Rabat na Morocco.