Aminiya:
2025-11-20@07:54:47 GMT

Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar Ansaru

Published: 20th, November 2025 GMT

Wata Kotun Tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 15 ga watan Janairun 2026, don fara shari’ar shugabannin ƙungiyar ’yan ta’adda ta Ansaru; Mahmud Usman da Abubakar Abba.

Ana zargin su da jagorantar ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, kuma Hukumar DSS ce ta kama su tare da gurfanar da su a kotu.

Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi Hakimi ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana

An tsara faea sauraren shari’ar a ranar Laraba, amma aka ɗage bayan lauyoyin waɗanda ake tuhuma sun nemi a ƙara musu lokaci.

Lauyansu, B.I. Bakum, ya bayyana cewa har yanzu suna jiran takardun zargi da wajen DSS.

Haka kuma, ya nemi a mayar da waɗanda ake tuhuma zuwa gidan gyaran hali domin suke samun damar ganawa da lauyoyinsu cikin sauƙi.

Lauyan DSS, David Kaswe, ya ƙi aminta da wannan buƙata.

Ya ce lauyoyin dole ne su rubuta wa DSS buƙatunsu kafin su ziyarci waɗanda ake tuhuma.

Alƙalin kotu, Emeka Nwite, ya yanke shawarar bai wa lauyoyin waɗanda ake tuhuma ƙarin lokaci domin shirya wa shari’ar.

Ya ce wannan zai tabbatar da adalci, sannan ya sanya ranar shari’a 15 ga watan Janairun 2026, domin fara sauraren shari’ar.

DSS, tana zargi waɗanda ake tuhuma da jagorantar kai harin gidan yarin Kuje da ke Abuja a 2022, inda fursunoni sama da 600 suka tsere.

Hakazalika, ta zarge su da kai hari wajen haƙar ‘uranium’ a Jihar Neja, tare da sace mutane da dama, ciki har da injiniyan ƙasar Faransa, Francis Collomp, a shekarar 2013.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ansaru kungiya Shari a zargi waɗanda ake tuhuma

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis

A ranar Alhamis, 20 ga watan Nuwamban 2025, ake sa ran Majalisar Wakilan Amurka za ta gudanar da zama na musamman domin bincikar zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya.

Kwamitin Majalisar Wakilan kan Afirka ya sanya ranar domin bitar fasalin da Shugaba Donald Trump ya yi kwanan nan na sanya Nijeriya a matsayin kasar da ake sa wa ido na musamman, CPC, kan zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi.

Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa, an gayyaci mambobin Kwamitin Harkokin Waje na majalisar, wanda aka shirya za a yi tattaunawar da misalin ƙarfe 11:00 na safe a Ɗaki mai lamba 2172 na Ginin Ofishin Gidan Rayburn, sannan kuma za a iya kalla ta intanet kai-tsaye, wanda wakili Chris Smith (R-NJ) ne zai jagoranta.

Za a gabatar da kwamitoci biyu na shaidu, ciki har da manyan jami’an Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da shugabannin addinai na Nijeriya.

Gayyatar tana cewa, “Ana roƙonku da girmamawa da ku halarci zaman sauraron ƙararraki na Kwamitin Harkokin Waje da ƙaramin kwamiti kan Afirka zai gudanar da shi da ƙarfe 11:00 na safe a ɗaki mai lamba 2172 na ginin Ofishin Rayburn House.”

Trump ne ya fara sanya Nijeriya a matsayin kasae da ake sa wa ido na musamman, CPC a shekarar 2020, kafin magajinsa, Shugaba Joe Biden, ya cire ƙasar daga jerin sunayen bayan ya kayar da Trump.

Masu sauraron za su haɗa da Babban Jami’in Ofishin Harkokin Afirka, Jonathan Pratt, da Mataimakin Mataimakin Sakatare na Ofishin Dimokuradiyya, ’Yancin Dan’Adam, da Aiki, Jacob McGee.

Za a yi zaman tattaunawa ta biyu da Daraktan Cibiyar ’Yancin Addini, Ms Nina Shea; Bishop Wilfred Anagbe na Makurdi Catholic Diocese a Nijeriya; da Ms Oge Onubogu ta Cibiyar Dabaru da Nazarin Ƙasashen Duniya.

Ana sa ran zaman tattaunawa ta majalisar zai sake duba girman zargin cuzguna wa masu wani addini a Nijeriya.

Za a kuma yi nazarin irin martanin manufofi da za a iya ɗauka, ciki har da takunkumin da aka yi niyyar ƙaƙabawa da taimakon jinƙai, da haɗin gwiwa da hukumomin Nijeriya don hana ƙarin tashin hankali.

Za a kuma gabatar da ƙudirin a gaban Majalisar Dattawan Amurka, wanda Sanata Ted Cruz ya ɗauki nauyinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Kotu A Gabon Ta Yanke Hukuncin Dauri A Kurkuku Kan Jami’an Tsohuwar Gwamnatin Kasar
  • An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari
  • Mai taɓin hankali ya kashe soja a Legas
  • Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a Kebbi
  • Najeriya ta Fara tattaunawa da Amurka kan zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin
  • Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai