Kasar Sin Na Nuna Damuwa Sosai Kan Harin Intanet Da Aka Kai Mata
Published: 4th, April 2025 GMT
A jiya Alhamis 3 ga wata ne, cibiyar daukar matakan gaggawa kan matsalolin kwayar cutar na’ura mai kwakwalwa ta kasar Sin, gami da ofishin gwajin ayyukan fasahohin magance kwayar cutar na’ura mai kwakwalwa na kasar, suka bullo da wani rahoto, kan binciken hare-haren yanar gizo da wasu kasashen waje suka kai kan tsarin adana bayanan gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta nahiyar Asiya karo na 9 da aka yi a birnin Harbin, babban birnin lardin Heilongjiang da ke arewa maso gabashin kasar Sin a shekara ta 2025, gami da wasu muhimman ababen sadarwa dake lardin na Heilongjiang, inda ya shaida yadda kasar Amurka ta kaddamar da hare-haren intanet, kan tsarin adana bayanan gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta Asiya karo na 9 da aka yi a birnin Harbin, gami da wasu muhimman ababen sadarwa na lardin Heilongjiang, kana ana kyautata zaton cewa hare-haren sun samu goyon-baya daga gwamnatin Amurka.
Har wa yau, yayin ziyararsa yankin Caribbean kwanan nan, sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Antonio Rubio ya ce wai hanyar mota da kasar Sin ta shimfida a kasar Guyana ba ta da inganci sam, inda Amurka ta yi fatan samar mata da zabi na daban. Game da wannan batu, Guo Jiakun ya ce, ba kamfanin kasar Sin ne ya shimfida waccan hanyar mota ba, kuma tuni Guyana ta karyata labarin. Kasar Sin na ganin cewa, maimakon shafa wa kasar Sin bakin fenti, da rura wutar rikici, gara Amurka ta aikata wa sauran kasashe alheri na zahiri. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
Wani saurayi ya wallafa wani labarinsa a kafar sada zumunta ta Reddit tare da yin nadama, inda ya ce matar da suke soyayya ta faɗa masa cewa, an haife ta ne a shekarar 1998, har sai da ya duba bayanan fasfo dinta.
A wani lamari mai ban al’ajabi da ban tsoro, matashin ɗan shekara 26 ya girgiza bayan ya gano cewa, matar da yake soyayya da ita da nufin aure, bayan shafe shekaru huɗu suna tare tana da shekara 47, ba 27 ba, kamar yadda ta yi iƙirari.
An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a ChibokSaurayin ya tafi shafin Reddit don ya wallafa labarinsa na nadama, inda ya ce, matar ta sha gaya masa cewa, an haife ta ne a watan Afrilun 1998, amma ya gano an haife ta a 1977 shekara 48 ke nan.
Saurayin ya rubuta a cikin shafin intanet cewa, “ina soyayya tare da budurwata har tsawon shekaru 4, kuma koyaushe tana ikirarin an haife ta a watan Afrilu ‘1998, amma na gano a ainihin lokacin da aka haife ta shi ne 1977.
Saurayin ya ce, ba shi da wani dalili na yin shakku, domin matar ta yi kama da ’yar shekara 27, ba wanda ya taba tunanin ta kusa 50 ba, amma ya yarda cewa akwai wasu alamomi a tsawon tafiyar soyayyar.
“Akwai wasu alamomi a lokacin da muke tare, amma na zabi in yi watsi da su tunda ba ni da gogewa kan gano ainihin (wannan ita ce alakar soyayya ta ta farko mai tsawo),” in ji shi, inda ya kara da cewa, matar ta damu da kamanninta, kuma duk kawayenta sun fi shekara 27 sosai.
“Duk lokacin da na nemi ta nuna min wasu takardu kamar fasfo sai ta ƙi nuna min, ta ba da uzuri na banza da kokarin kauce wa batun.”
A yayin binciken, saurayin ya kuma sami hoton gwajin ciki, wanda ’yan watanni kafin su hadu kuma su fara soyayya.
Kafofin sada zumunta na zamani sun mayar da martani kan batun, yayin da sakonni suka yi ta yaduwa, daruruwan mutane sun sharhi, inda akasari ke fada wa mutumin ya kawo karshen dangantakarsa da matar da aka gina ta bisa karya.