Aminiya:
2025-07-30@21:49:28 GMT

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

Published: 30th, July 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wasu al’ummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi tsarin yin gwajin lafiyar ma’aurata kafin a daura musu aure.

A wasu lokutan, akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure. Matsalolin sun hada da yaduwar cututtuka, samun ‘ya’ya marasa lafiya da sauran wasu matsalolin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu alummomin suka rungumi yin gwajin jini kafin aure.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwajin jjini

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga

Kwamitin Majalisar Dattawa na bin Diddigi ya ba Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) wa’adin mako uku ya amsa tambayoyi kan rashin ba da ba’asi kan Naira tiriliyan 210 da ba a san inda suka shiga ba daga shekarar 2017 zuwa 2023.

An dai bayar da wa’adin ne ga shugaban kamfanin na kasa, Bayo Ojulari, wanda ya bayyana a gaban kwamitin ranar Talata, bayan ya bayar da hakuri kan rashin bayyanarsa yayin gayyatar da kwamitin ya yi masa a baya.

Yadda ’yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF

Kwamitin, wanda ke karkashin jagorancin Ahmed Wadada Aliyu (Nasarawa), ya tsaya kai da fata cewa dole kamfanin ya bayyana inda kudaden suka shiga.

Ojulari dai ya ba kwamitin hakuri, inda ya ce yana bukatar karin lokaci kafin ya iya amsa tuhumar da aka yi masa har guda 19.

Ya kuma ce, “Da kadan na haura kwana 100 a matsayin shugaban wannan kamfanin. Ina bukatar karin lokaci kafin na iya zakulo bayanan da kuka bukata. Wannan kuma na zuwa ne a daidai lokacin da sauran tarin ayyuka ke jira na.

“Ni kaina ina bukatar fahimtar abubuwan da kaina kafin na iya bayar da amsa a kansu. Amma zan je na zauna da sauran ma’aikatana da suka dace mu tattauna domin bayar da abin da ake bukata,” in ji shugaban na NNPCL.

Kodayake mako hudu ya bukata, amma kwamitin ya ba shi mako uku ne domin ya gabatar da bayanan.

Da yake karin haske a kan kudaden, Sanata Wadada ya ce kudaden da ake magana a kan su rubi biyu ne, akwai Naira tiriliyan 103 da kuma Naira tiriliyan 107 da suke bukatar bayanan a kan su.

“Amma fa ba mu ce wadannan kudaden da ake magana a kan su sace su aka yi ko kuma sun bace ba. Abin da kwamitinmu kawai yake kokarin yi shi ne bincike domin gano yadda aka yi tusarrufi da su,” in ji Sanata Wadada.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Kissoshin Kayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 122
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almutaba (a) 120