Jakadan kasar Iran a cibiyoyin MDD a kasashen Turai ko Geneva Ali Gahraini ya yi tir da amincewar da hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD ta yi da zargin kasar ta take hakkin bil’adama a taronta na baya-bayan nan abirnin Geveva.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baraini yana cewa, hukuncin da hukumar ta yanke a kan JMI na son zuciya ne kuma saboda siyasar JMI a duniya ne.

Bahraini ya kara da cewa, wannan hukuncin ya taba mutucin hukumar ta yin adalci ga wasu kasashen a duniya.

Bahraini ya kara dan cewa, abin mamakoi shigha ba’a taba jin wannan hukumar ta yankewa HKI irin wannan hukuncin ba, duk tare da cewa duk duniya tana ganin yadda take keta hakkin Falasdinawa tun shekara ta 2023.

Jakadan ya kara da cewa ‘sunan da hukumar ta bawa bincike da kuma hukuncinta wato (Kare Hakkin Bil’adama a JMI) da kuma sakamakon da ta fitar ya tabbatar da kariyar wannan hukumar, sannan ya zubar da mutuncin hukumar a idon kasashen duniya da dama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura

Akalla mutane 7 ne aka ceto, bayan kifewar kwale-kwale a wani kogi da ke Zangon Maje, ƙaramar hukumar Taura, ta jihar Jigawa ranar Litinin.

Shugaban ƙaramar hukumar Taura, Dr Shuaibu Hambali ne ya bayyana hakan ga Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, lokacin da wasu manoma ke dawowa daga gonakinsu a ƙauyen Zangon Maje, inda suka hau kwale-kwalen.

Ya ce, jami’an bada agajin gaggawa  na yankin sun samu nasarar ceto mutane 7 a kokarin da suka yi na ceto wadanda lamarin ya shafa.

Ya ƙara da cewa, masu ceton sun gano gawar mutum guda a yankin Yalleman da ke ƙaramar hukumar Kaugama.

Dr Shuaibu ya bayyana cewa, sauran mutane 9 da ke cikin jirgin har yanzu ba a same su ba a lokacin da ake bayar da wannan rahoto.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, ba a fitar da sunayen waɗanda abin ya shafa ba, amma lamarin ya jefa al’ummar yankin cikin jimami da baƙin ciki.

Shugaban ƙaramar hukumar ya bayyana cewa, za a raba rigunan kariya (life jacket) ga fasinjoji a nan gaba kadan domin kiyaye sake afkuwar lamarin nan gaba.

Ya kuma gargadi matuka kwale-kwale da su kiyaye ƙa’idojin tsaro da kaucewa cunkoson fasinjoji, musamman da yamma a lokacin damina, inda ruwa ke  ƙaruwa a kowane lokaci.

Dr Hambali, wanda ya isa wurin da abin ya faru, ya jajanta wa iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Wasu daga cikin mazauna yankin da Rediyon Najeriya ta tattauna da su, sun nemi gwamnatin ta gaggauta ɗaukar matakan da suka dace, tare da inganta hanyoyin sufuri ta ruwa.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya