Bello Turji ya kashe manoma 11 a wani sabon hari a Sakkwato
Published: 3rd, April 2025 GMT
Ƙasurgumin ɗan bindiga, Bello Turji, da mayaƙansa sun kai mummunan hari garin Lugu da ke Ƙaramar Hukumar Isa a Jihar Sakkwato, inda suka kashe manoma 11.
Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru ne yayin da Turji ke dawowa daga wata ziyarar sallah da ya kai yankin.
Najeriya ta yi kuskuren barin Boko Haram ta yi ƙarfi — Muftwang NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ‘Ya’yansuWani mazaunin Isa, Basharu Altine Giyawa, ya ce, “Tun a ranar Asabar muka samu bayanai cewa Turji zai ziyarci Gatawa, kuma mun sanar da hukumomi.
“Duk da haka, shi da mutanensa sun bi ta ƙauyukanmu, sun yi bikin sallah, sannan suka kashe manoma 11 a hanyarsu ta komawa Fakai.”
Ɗan majalisar dokokin Jihar Sakkwato mai wakiltar yankin, Hon. Aminu Boza, ya tabbatar da samun rahoton harin.
Amma ya ce: “Turji bai ziyarci kowace unguwa a yankina domin yin sallah ba. Mun ɗauki matakin gaggawa bayan samun bayanai, wanda hakan ka iya zama dalilin da ya sa ya mayar da martani kan waɗannan manoman a Isa.”
Mazauna yankin sun bayyana damuwa kan yadda hare-haren ‘yan bindiga ke ci gaba da ƙaruwa, duk da ƙoƙarin jami’an tsaro.
Sun yi kira ga gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen magance matsalar domin kare rayuka da dukiyoyinsu.
Hukumomin tsaro har yanzu ba su fitar da wata sanarwa kan harin ba, amma majiyoyi sun bayyana cewa sojoji na bin sahun Turji domin daƙile ayyukansa a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Bindiga hari Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
Jami’an diflomasiyya a Tanzania sun ce akwai kwararan hujjoji da ke tabbatar da an kashe akalla mutum 500 a cikin kwana biyu da barkewar zanga-zangar kin amincewa da sakamakon zaben da aka gudanar a ranar Laraba.
Sai dai a wani bangaren kuma, alkalumman Yan’adawa sun zarta haka.
Wakiliyar BBC ta ce ministan harakokin wajen Tanzania Mahmoud Kombo Thabit ya musanta rahotannin, amma wani jagoran adawa John Kitoka ya ce ‘yansanda da wasu sojojin haya na kasashen waje ne suka aiwatar da kisan mutane cikin dare.
Majalisar Dinkin Dauniya ta yi kiran gudanar da bincike kan zargin amfani da karfin da ya wuce kima a kan masu zanga-zangar.
BBC