Tinubu zai halarci jana’izar mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC a Filato
Published: 4th, October 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai tashi daga Legas zuwa Jos, Babban Birnin Jihar Filato, a ranar Asabar domin halartar jana’izar mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nantewe Yilwatda Goshwe.
Zai halarci jana’izar Nana Lydia Yilwatda Goshwe, mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa.
Bayo Onanuga, Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, ya ce Shugaban Ƙasa zai kuma gana da shugabannin coci daga Arewacin Najeriya a Jos.
Ana sa ran Tinubu zai koma Legas a ranar bayan kammala ziyarar.
A gefe guda kuma, Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato ta sanar da taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a Jos da Bukuru saboda ziyarar TIinubu.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Rt. Hon Joyce Lohya Ramnap, ya ce za a rufe wasu manyan hanyoyi daga ƙarfe 7 na safiyar ranar Asabar domin bai wa tawagar Shugaban Ƙasa damar yin zirga-zirga ba tare da matsala ba.
Hanyoyin da abin zai shafa sun haɗa da:
1. Mararaban Jama’a zuwa babbar hanyar Bukuru
2. Dadin-Kowa, Tsohon Filin Jirgi zuwa shataletalen Filato
3. Shataletalen Hillstation zuwa Hedikwatar COCIN/Central Bank road
Gwamnati ta roƙi al’umma da masu ababen hawa su yi haƙuri tare da haɗin kai, inda ta bayyana waɗannan matakan a matsayin na wucin gadi don tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali yayin ziyarar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ziyara Shugaban Ƙasa
এছাড়াও পড়ুন:
Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%
An samu wannan raguwar ne sakamakon sauye-sauyen da aka samu a shekarar da muke ciki.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA