Aminiya:
2025-11-18@14:04:50 GMT

Tinubu zai halarci jana’izar mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC a Filato

Published: 4th, October 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai tashi daga Legas zuwa Jos, Babban Birnin Jihar Filato, a ranar Asabar domin halartar jana’izar mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nantewe Yilwatda Goshwe.

Zai halarci jana’izar Nana Lydia Yilwatda Goshwe, mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa.

Ana fargabar mutuwar mutane a gobarar tankar mai Boko Haram ta wuce yadda mutane ke tsammani — Jonathan

Bayo Onanuga, Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, ya ce Shugaban Ƙasa zai kuma gana da shugabannin coci daga Arewacin Najeriya a Jos.

Ana sa ran Tinubu zai koma Legas a ranar bayan kammala ziyarar.

A gefe guda kuma, Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato ta sanar da taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a Jos da Bukuru saboda ziyarar TIinubu.

Kwamishinan Yaɗa Labarai, Rt. Hon Joyce Lohya Ramnap, ya ce za a rufe wasu manyan hanyoyi daga ƙarfe 7 na safiyar ranar Asabar domin bai wa tawagar Shugaban Ƙasa damar yin zirga-zirga ba tare da matsala ba.

Hanyoyin da abin zai shafa sun haɗa da:

1. Mararaban Jama’a zuwa babbar hanyar Bukuru

2. Dadin-Kowa, Tsohon Filin Jirgi zuwa shataletalen Filato

3. Shataletalen Hillstation zuwa Hedikwatar COCIN/Central Bank road

Gwamnati ta roƙi al’umma da masu ababen hawa su yi haƙuri tare da haɗin kai, inda ta bayyana waɗannan matakan a matsayin na wucin gadi don tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali yayin ziyarar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ziyara Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

 

An samu wannan raguwar ne sakamakon sauye-sauyen da aka samu a shekarar da muke ciki.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai ‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga  November 17, 2025 Labarai Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi November 17, 2025 Labarai MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi November 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PDP Ba Ta Mutu Ba Duk Da Rikicin Da Ta Ke Fama Da Shi – Anyanwu
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%
  • Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 
  • ’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato
  • Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang
  • Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa
  • Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso