Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Fintiri ya yi watsi da korar Wike daga PDP

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na Jihar Adamawa, ya yi watsi da hukuncin da Jam’iyyar PDP ta yanke na korar Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, daga jam’iyyar.

Aminiya ta ruwaito yadda PDP ta kori Wike, Sanata Samuel Anyanwu da tsohon Gwamnan Ekiti, Ayodele Fayose, a yayin babban taron PDP da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo.

Cif Olabode George ne, ya gabatar da ƙudirin korarsu, kuma Shugaban PDP na Jihar Bauchi, Samaila Burga, ya mara masa baya.

Sai dai bayan sanarwar, Gwamna Fintiri ya fitar da wata sanarwa, wadda ya nesanta kansa daga matakin da jam’iyyar ta ɗauka.

Ya ce ba ya goyon bayan korar da aka yi wa Wike, domin hakan zai ƙara haifar da rikici a cikin jam’iyyar.

“Ina son na bayyana a fili cewa ba na goyon bayan korar Ministan Babban Birnin Tarayya, Wike daga PDP. Wannan mataki ba zai amfani jam’iyya ba. Ba zan shiga cikin abin da zai ƙara ruguza jam’iyya ba,” in ji shi.

Fintiri, ya ce yana ganin zaman lafiya da haɗin kai sun ɗore a jam’iyyar PDP.

Ya roƙi ’ya’yan jam’iyyar da su mayar da hankali kan yin sulhu maimakon ƙara haddasa rikice-rikice.

“Na yi imani cewa sulhu da fahimtar juna su ne hanyar da ta fi dacewa. Ina kira ga kowa ya yi aiki don ganin an samu haɗin kai a cikin jam’iyya.”

Fintiri, na cikin gwamnoni huɗu da suka halarci taron, kuma shi ne Shugaban Kwamitin Shirya Taron.

Gwamnonin Jihar Osun, Ademola Adeleke; Taraba, Agbu Kefas; da Ribas, Siminalayi Fubara ba su halarci taron ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu shigar da kara na ICC sun bukaci hukuncin daurin rai da rai a kan kwamandan RSF
  • Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty
  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin
  • Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 
  • Shugaban Nukiliyar Iran Yace Amurka Da Israila Sun Shiga Sabon Mataki Mai Hadari
  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • Lebanon za ta shigar da kara a kan Isra’ila a MDD game da gina Katanga a iyakarta
  • Fintiri ya yi watsi da korar Wike daga PDP
  • Ma’ariv: Netanyahu Yana Tsoron Hukuncin  Da Kotu  Za Ta Yanke Akansa