Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara
Published: 2nd, October 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.কীওয়ার্ড: Kwara Masu Garkuwa Da Mutane
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
’Yan sanda sun yi nasarar kama wasu ’yan bindiga biyar tare da ƙwace tarin makamai a hannunsu a yankin Zuru–Tadurga da ke Jihar Kebbi.
Rundunar ’yan sanda ta musamman da ta kama su, ta bayyana cewa, ’yan bindiga suna cikin waɗanda suka kai hare-hare a kan al’ummomin Zuru a kwanakin baya.
Ta ƙara da cewa dukkansu ’yan asalin kauyen Birnin Tudu ne da ke cikin ƙananan hukumomin Bukkuyum da Gummi a Jihar Zamfara.
Kakakin ’yan sanda a jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce makaman da aka ƙwato daga hannun ’yan bindigar sun haɗa bindigogi AK-47 guda 7 a wata ƙaramar gida guda 1 da harbi-ruga guda uku.
’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh GumiSauran sun haɗa da kurtun albarusan AK-47 guda 3 da harsashi 89 da kuma tsabar kuɗi Naira miliyan 2.6
Ya ƙara da cewa an miƙa waɗanda ake zargin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Birnin Kebbi domin ci gaba da bincike da kuma gano sauran abokan aikinsu.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya yaba da jarumta da jajircewar jami’an rundunar tare da ƙarfafa su da kada su yi ƙasa a gwiwa har sai an kawar da matsalar ’yan bindiga da garkuwa da mutane daga jihar.