Leadership News Hausa:
2025-11-18@14:02:58 GMT

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

Published: 30th, September 2025 GMT

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

An sanar da wannan matakin ne a yau 29 ga watan Satumba, 2025 a karkashin dokokin FIFA, amma kuma har yanzu SAFA suna da kwanaki goma domin daukaka kara a gaban kwamitin daukaka kara na FIFA.

 

Tawagar Afirka Ta Kudu wadda Hugo Broos ke jagoranta a halin yanzu suna kan gaba a rukuninsu na C na neman cancantar shiga gasar cin kofin duniya, bayan da suka samu maki 17 daga wasanni takwas, amma kuma yanzu makin ya rikito zuwa 14 sakamakon zabtare maki 3 da hukumar FIFA ta yi musu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

CAF ta fitar da ’yan wasa uku da suka rage a takarar gwarzon Afirka na bana

Hukumar ƙwallon ƙafar Afirka CAF, ta bayyana cewa bayan tankade da rairaya da ta yi, a yanzu ’yan wasa uku kacal ne suka rage a takarar gwarzon nahiyyar na bana.

A wata sanarwar da hukumar ta fitar a ranar Lahadi, ta bayyana Achraf Hakimi da Mohamed Salah da Victor Osimhen, a matsayin sauran ukun da suka rage a takarar gwarzon dan ƙwallon ƙafar Afirka na bana.

Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno

Hakimi, kyaftin din Morocco, ya lashe kofuna daga ciki har da Champions League a PSG — na farko a tarihin ƙungiyar — da Ligue 1, da European Super Cup, da kuma kai wa zagayen ƙarshe a FIFA Club World Cup da Chelsea ta lashe a Amurka.

Shi kuwa Mohammed Salah ya taka rawar gani a Liverpool a kakar da ta wuce da lashe Premier League, kuma shi ne kan gaba a zazzaga kwallaye mai 29 da bayar da 18 aka zura a raga, hakan ya sa ya karbi kyautar takalmin zinare, wato Golden Boot.

Mohammed Salah dan ƙasar Masar mai shekara 33 na fatan karbar kyautar gwarzon Afirka karo na uku bayan 2017 da kuma 2018.

Shi kuwa dan ƙwallon tawagar Super Eagles ta Najeriya, Victor Osimhen ya jagoranci Galatasaray ta dauki babban kofin tamaula na Turkiya da cin ƙwallo 26.

Osimhen ya taba zama gwarzon Afirka 2023 a lokacin da shi kuma Hakimi ya yi na biyu

To sai dai mai riƙe da kyautar a yanzu, wato Ademola Lookman na Nijeriya, bai kai bante ba a kakar nan sakamakon gaza taka rawar gani yadda ake buƙata.

Za a gudanar da bikin karrama gwarzon dan ƙwallon ƙafa na Afirka na bana ranar Laraba a birnin Rabat na Morocco.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-yanzu: Fada ya barke a Hedikwatar Jam’iyyar PDP
  • CAF ta fitar da ’yan wasa uku da suka rage a takarar gwarzon Afirka na bana
  • Na’ini: Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Da Kansa Ya Jagoranci Yaki Kwanaki 12 Da Aka Kaddamar Kan Iran
  • Afirka ta Kudu na Binciken shigar wasu ‘yan gudun hijirar Falasdinu 153 cikin kasar
  • Najeriya ba za ta buga kofin duniya ba karo na biyu a jere
  • An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing
  • Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30
  • Lebanon za ta shigar da kara a kan Isra’ila a MDD game da gina Katanga a iyakarta
  • Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca
  • Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi