Xi: Ya Kamata A Sa Kaimi Ga Dunkulewar Addinan Sin Da Kyawawan Al’adun Gargajiya Na Kasar
Published: 29th, September 2025 GMT
Da yammacin yau Litinin ne ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya gudanar da taron nazari karo na 22, kan yadda za a sa kaimi ga mayar da addinan Sin zuwa addinan dake da salo na kasar.
Yayin da ya jagoranci taron, babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya jaddada cewa, “Ya kamata mu tattara, da kuma amfani da darussan tarihi, mu mayar da hankali kan hakikanin ayyukan addinai na kasa, da sa kaimi ga mayar da addinan Sin zuwa addinan dake da salo na kasar, da kuma jagorantar addinai don daidaita al’umma mai ra’ayin gurguzu”.
Xi Jinping ya kara da cewa, ana bukatar sa kaimi ga dunkulewar addinan kasar Sin, tare da kyawawan al’adun gargajiya na kasar bisa wayewar kan al’ummar kasar na tsawon shekaru dubu 5, da kuma karfafa fahimtar ma’aikatan dake gudanar da harkokin addinai, da masu bin addinai, kan amincewa da al’adun kasar Sin.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30
Yanzu haka ana gudanar da taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayin duniya ta Majalisar Dinkin Duniya, karo na 30, wato “COP 30” a takaice, a birnin Belem na kasar Brazil, inda a ranar Juma’a 14 ga wata aka kira wani taro a gefe mai taken “Dabarun Kasar Sin Na Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya”, don bayar da fasahohin Sin a fannin daidaita al’amura a kokarin sabawa da sauyin yanayi.
A wajen taron, shugaban tawagar kasar Sin a taron COP30, kana mataimakin ministan muhallin halittu na kasar, Li Gao, ya ce sauyin yanayin duniya wani babban kalubale ne da daukacin bil Adama ke fuskantarsa, inda a nata bangare, kasar Sin ta tsaya kan mai da hankali kan dukkan bangarorin dakatar da sauyin yanayi, da kokarin sabawa da shi. Kana kasar tana gudanar da gwaje-gwaje a biranenta 39 ta fuskar daidaita tsare-tsare don sabawa da sauyin yanayin duniya. Ban da haka, jami’in ya ce, kasar Sin na son karfafa hadin gwiwa tare da sauran kasashe, a kokarin tinkarar sauyin yanayi, da inganta fannin sabawa da sauyin yanayin duniya a kasashe daban daban.
Duk dai a wajen taron, Francesco Corvaro, wakilin kasar Italiya mai kula da batun sauyin yanayi, ya yi yabo ga kasar Sin bisa nasarorin da ta samu a kokarin sabawa da sauyin yanayin duniya, inda ya ce ci gaban da kasar Sin ta samu ya nuna makomar aikin tinkarar sauyin yanayi a duniya, kuma yana sa ran ganin Sin ta zama tamkar wata gada mai hada dukkan bangarorin kasashe masu tasowa da masu sukuni, ta yadda za a tabbatar da hadin gwiwar daukacin bil Adama a kokarin tinkarar sauyin yanayin duniya. (Bello Wang)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA