Aminiya:
2025-06-20@20:35:47 GMT

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa 

Published: 25th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wani sabon ango, sun kuma yi wani gaba da amaryasa bayan kwanaki 11 da ɗaura aurensu a wata unguwa a Jihar Nasarawa.

Ganau sun shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun kai hari gidan sabbin ma’auratan ne da misalin ƙarfe karfe 11:00 na dare ranar Laraba, inda suka harbe angon har lahira, sannan suka tafi da matar zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Name(required) Email(required) Website Message

Submit

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Akaleku, da ke Ƙaramar Hukumar Obi ta Jihar Nasarawa, a kan hanyar Lafia zuwa Makurɗi.

Ma’auratan, Mista da Misisi Alu Anzaku, an ɗaura aurensu ne a ranar 12 ga Afrilu, 2025.

An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure

Majiyoyi masu kusanci da iyalan ma’auratan sun ce da alama suna cikin lokacin amarci lokacin da wannan mummunan lamari ya faru, wanda ya katse sabuwar rayuwarsu tare.

Har zuwa lokacin da ake haɗa wannan rahoto, ’yan uwa da abokan arziki sun ci gaba da nuna matukar damuwa, saboda har yanzu ba a samu wani labari game da inda amaryar da aka sace take ba, ko kuma halin da take ciki.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ba amsa kiran waya da sakonnin tambayoyin da wakilimmu ya aika mata game da lamarin ba har zuwa lokacin da aka kammala rubuta wannan labarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Amarya Ma aurata

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.

 

Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.

 

Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.

 

Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
  • Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna