HausaTv:
2025-11-23@04:40:37 GMT

Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar

Published: 15th, March 2025 GMT

Amurka ta baiwa jakadan Afrika ta Kudu a kasar wa’adin sa’o’i 72 na ya san idna dare ya yi masa.

Hakan dai na zuwa ne bayan da Amurkar ta ce ba ta maraba da Jakadan na Afirka ta Kudu a kasar Ebrahim Rasool.

 Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya zargi jakadan da na Afrika ta Kudu da nuna “kiyayya” ga shugaban Amurka Donald Trump.

Marco Rubio ya ce Ambasada Ebrahim Rasool “yana kara ruruta wutar rikicin kabilanci kuma gwamnatin Trump ba ta da wani abin da za ta ce masa.”

Tuni Fadar shugaban kasar Afirka ta Kudu ta mayar da martani inda ta ce ta yi na’am da matakin.

Sanarwar ta ce “abin takaici ne korar jakadan na Afirka ta Kudu a Amurka” inda “ta kuduri aniyar kulla alaka mai amfani da moriyar juna” da Washington.

Rahotannin sun ce jakadan ya bayyana a wata cibiyar nazari ta Afirka ta Kudu inda ya yi ikirarin cewa yunkurin Trump na Make America Great Again, tare da tasirin Elon Musk da mataimakin shugaban kasa JD Vance, wani bangare ne na al’amuran duniya na fifita farar fata.

Dama dai dangantaka tsakanin Amurka da Afrik ata kUdu ta yi tsami sakamakon matsayin Pretoria kan hakkin Falasdinu.

Kasar Afrika ta Kudu dai ta kasance kan gaba a shari’ar da kotun kasa da kasa ta ICJ ke yi na zargin gwamnatin Isra’ila da kisan kiyashi a Gaza.

A watan da ya gabata ne dai fadar White House ta sanar da dakatar da tallafin da Amurka ke baiwa Afirka ta Kudu a matsayin martani ga karar Afirka ta Kudu da ke gaban kotun ICJ.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Sanar Da Nada Janar Jahanshashi A Matsayin Kwamandan Dakarun Rudunar Sojin Kasa

Rahotanni sun bayyana cewa an sanar da sunan brigadier janar Ali Jahanshashi a matsayin sabon kwamandan dakarun sojan kasar iran inda ya gaji brigadier janar Kiumars Haidari

Bayanan da yayi jim kadan bayan sanar da nadin nasa a yau Asabar, Jahanshahi ya jaddada cewa dakarun sojin kasar a shirye suke su mayar da martani kan duk wata barazana ta hanyar amfani da kwarewarsu da makamai na zamani da kuma daukan darasi kan rikicin da ya faru abaya bayan nan musamman yakin kwanaki 12 da Israila ta kallafa mata.

Haka zalika ya kara da cewa a halin yanzu sojoji sun bada fifiko ga kaidoji da dokoki guda 5 da jagoran juyin musulunci na iran Ayatullah imam khamnai ya sanya, wanda suka mayar da hankali kan iganta matakin kariya da karfin dan adam da nagarta da kayan aiki don mayar da martani kan duk wata barazana da za ta taso.

Daga karshe ya bayyana cewa bisa shiryarwar jagoran musulunci kan hadinkan alummar iran da karfin sojin kasar za’a iya murkushe duk wani makircin da makiya suke kullawa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Bukaci shugaba Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000 November 22, 2025 Nijar:  Dubban Mutane Sun Tarbi Janar Thiani Bayan Komarwa Birnin Yamai November 22, 2025  Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba November 22, 2025 Rundunar Sojan Iran Tana Cikin Shirin Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana November 22, 2025  Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka November 22, 2025 Unifil: Girmama Hurumin Kasar Lebanon Ne Ginshikin Kuduri Mai Lamba 1701 November 22, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 160 November 22, 2025 Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA November 22, 2025 Ghalibaf: Makiya Sun Sawya Dabarbarun Yaki Da Iran November 22, 2025 Tsohon Ma’aikacin CIA Ya Ce HKI Ta Yi Barazanar Amfani Da Makaman Nukliya Kan Iran November 22, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar
  • Iran Ta Sanar Da Nada Janar Jahanshashi A Matsayin Kwamandan Dakarun Rudunar Sojin Kasa
  •  Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Yan Majalisar Dokokin Amurka Sun Sami Rarrabuwar Kai Dangane Da ‘Keshe Kiristoci A Najeriya’
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • DSS ta mayar da Nnamdi Kanu gidan yarin Sakkwato
  • Shugaban Rasha yace Ba zai Janye Ayyukan Soji  Da Yake Yi A Kasar Ukrain Ba
  • Amurka ta Shawarci Ukraine ta amince da yankunan da Rasha ta mamaye mata
  • Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar