HausaTv:
2025-07-05@22:30:29 GMT

Rasha Za Ta Kara Yawan Alkamar Da Take Kai Wa Kasashen Afirka

Published: 15th, March 2025 GMT

Cibiyar da take fitar da amfanin gona zuwa waje ta kasar Rasha, ta sanar da cewa; a cikin shekarar 2024 an sami karuwar kayan abincin da take fitarwa zuwa wasu kasashen Afirka da kaso 19% da kudin da su ka hau da dala biliyan 7.

Wasu kasashen da Rashan za ta linka yawan alkamar da take aikewa su ne Moroko, Najeriya da kuma Kamaru.

Yawan alkamar da kasar Rashan za ta aike zuwa Moroko ta kai ton 124,000,a 2024 kuwa yawan alkamar da ta aikewa ita ton 54,000.

Ita kuwa kasar Najeriya yawan alkamar da Rashan ta aike mata ta tashi daga ton 48,000 zuwa ton 131,400.

Alama ce muhimmin kayan abincin da kasar Rasha take aike wa nahiyar Afirka. A shekarar 2024 da ta gabata ta kai wa nahiyar alkama da kudinta su ka kai dala biliyan 7.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

A yau Asabar ne ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwaran aikinsa na kasar Ghana Samuel Okudzeto Ablakwa, suka aikewa juna sakon murnar cika shekaru 65, da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

A cikin sakonsa Wang Yi ya bayyana cewa, cikin shekaru 65, an raya dangantaka tsakanin Sin da Ghana yadda ya kamata, kana an karfafa imani da juna kan harkokin siyasa, tare da samun manyan nasarori a hadin gwiwarsu ta fannoni daban daban. Kazalika, sassan biyu sun goyi bayan juna a fannin kulawa da harkokin kasa da kasa.

Wang Yi ya ce, ana fatan yin kokari tare da minista Ablakwa, wajen kara fadada mu’ammala a tsakanin ma’aikatun harkokin wajen kasashen biyu, da goyon bayan juna, da aiwatar da manufofi da aka amince da su, a gun taron koli na Beijing, na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, don sa kaimi ga daga dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da Ghana zuwa sabon matsayi.

A nasa bangare, minista Ablakwa ya bayyana cewa, kasar Ghana na godewa Sin, bisa samar mata da gudummawa, da goyon baya a fannonin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Ya ce an samu manyan nasarori a fannin hadin gwiwar sassan biyu karkashin tsarin dandalin FOCAC, wanda hakan ya samar da babbar gudummawa ga kasashen Afirka ciki har da Ghana, wajen inganta karfinsu na samun ci gaba, kuma hakan zai amfani jama’ar kasashen Afirka baki daya. Bugu da kari, kasar Ghana tana fatan kokartawa tare da kasar Sin, wajen sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare yadda ya kamata. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
  • Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
  • Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • An Bude Mafiya Yawan Tashoshin Jiragen Sama A Iran Bayan Tsaida Yaki
  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan