Jerin Gwarazan Taurarinmu
Published: 1st, November 2025 GMT
3. A Hangen Nesansa wajen jagorancin al’umma, ya mayar da hankali kan masana’antu, sabunta ababen more rayuwa da kuma gina Dan’adam; domin mayar da Jihar Nasarawa matsayin wata babbar cibiyar zuba jari a Nijeriya da horar da aikin injiniya tare da kyautata jin dadin al’ummar jihar; an zabi Injiniya Abdullahi A.
Injiniya Abdullahi Sule: Wanda Ya Fi Yin Fice Kan Harkokin Masana’antu A Duk Fadin Arewa
4. Shugabancinsa ya yi matukar kawo sauye-sauye a Jihar Ekiti, musamman ta hanyar gudanar da mulki na adalci, sabunta ayyukan more rayuwa, karfafa matasa da fadada aikin gona; sakamakon tawali’un da yake da shi da horon da ya samu wajen tafiyar harkokin kudi da gina jama’a tare kuma karfafa al’adun demokuradiyya; ya sa aka zabi Biodun Abayomi Oyebanji a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.
Biodun Abayomi Oyebanji: Wanda Ya Kawo Juyin-juya-hali A Jihar Ekiti
5. A sauyin da ya kawo a shugabancinsa, jajircewarsa na kawo ci gaba a fannin tsaro, zuba jari mai yawan gaske a fannin ilimi, kiwon lafiya da sauran ababen more rayuwa; kazalika a kokarinsa na sake mayar da Jihar Zamfara kan turbar zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, Dauda Lawal shi ne Gwarzon Gwamnanmu na wannan shekara.
Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
6. Ya dukufa wajen mayar da hankali kan manufar da ya sanya gaba, mai taken; “MORE Agenda”, wanda ya sake fasalin tsarin mulkin Jihar Delta ta hanyar zaman lafiya, hadin kai da kuma jajircewa wajen samar da ababen more rayuwa, ilimi, lafiya da kuma gina al’adun jama’a bisa gaskiya, tsantseni a sha’anin harkar kudi ta bangarori da dama; Rt. Hon. Sheriff Oborebwori, shi ne gwarzon gwamnanmu na 2025.
Sheriff Oborebwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma
7. Saboda kasancewarsa mai sasanta mutane da hada kansu duk da bambance- bambancensu; ga kuma samar da abubuwan more rayuwa a kauyuka, farfado da lamarin kula da lafiyar al’umma, taimaka wa manoma da matasa yadda za su tsaya da kafafunsu; tafiyar da gwamnati ta tausaya wa al’umma, yin biyayya da dokoki, da tunanin yadda gaba za ta yi kyau; shi ya sa aka zabi Sanata Uba Sani a matsayin Gwarzon Gwamnan shekarar 2025.
Sanata Uba Sani: Mai Hada Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu
Gwarzon Dan Majalisa Na Shekarar 2025
8. Saboda yadda ya shahara wajen yin doka, wakilci, nuna damuwa da sai abu ya kasance; yadda yake da hazaka, sa ido kan ci gaban inda yake wakilta, da kokarin samar da zaman lafiya, tsarin da ya sa aka samu cimma buri a gyaran tsarin mulki, hadin kan kasa;. Honorabul Benjamin Okezie Kalu, PhD, CFR don haka shi ne dan majalisar shekarar 2025.
Benjamin Okezie Kalu: Wakili A Majalisa Saboda Hadin Kan Kasa, Zaman Lafiya, Da Ci Gaba
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025
9. Bisa la’akari da yadda ya tafiyar da sha’anin kawo gyara a lamarin tara haraji, abin da aka aiwatar ta yadda ya dace a yi da gaskiya domin habbaka hanyoyin samun kudaden shiga ba ta hanyar man fetur ba, amma ta hanyar bullo da wasu dabaru ta kafar sadarwa ta zamani; da yake an dauki hukumomin gwamnati da su ma abokan tafiya ne domin samun ci gaba, ba tare da an sa wani abu na matsi ba; Dakta Zacch Adedeji a yanzu shi ne gwarzon ma’aikakaci na shekarar 2025.
Dakta Zacch Adedeji: Wanda Ya Kara Daukaka Darajar Haraji A Nijeriya
Gwarzon Dan Kasuwa Na 2025
10. Saboda hangen nesansa wajen kawo gyara a lamarin bunkasa samar da takin zamani a Nijeriya da kuma harkar kasuwancin amfanin gona; don tallafa wa miliyoyin manoma hanyar amfani da abubuwan gida. Da kuma kokarinsa na samar da wata hanyar taimakawa masu karamin karfi yadda za su cimma burinsu na maida aikin gona a matsayin wata hanya da za ta taimaka wa al’umma; don haka Thomas Etuh shi ne gwarzon Dan kasuwa na shekarar 2025.
Thomas Etuh: Gwarzo Wajen Samar Da Hanyoyin Dogaro Da Kai Ga Matasa
Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025
11. Domin jagorantar bangaren hakar mai da iskar gas na tekun Nijeriya da ya yi nasarar samar da ganga miliyan 1.8 na man fetur a kowace rana; da kuma jagorantar hukumar NUPRC ta zarce burinta na samun kudaden shiga da kashi 84.2 cikin dari, Injiniya Gbenga Komolafe shi ne Gwarzon Shugaban Kamfani na Shekara ta 2025.
Gbenga Olu Komolafe: Jagorantar Tsarin Samar Da Makamashi A Nijeriya
Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025
12. Domin jagorantar harkar kudi ta hanyar kirkire-kirkire tare da karfafa samar da kanana da matsakaitan sana’o’i (MSME) 700,000 da karfafa tubalin tattalin arzikin Nijeriya da kuma sake fasalta banki; an zabi Dakta Tony Okpanachi a matsayin Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025.
Dr Tony Okpanachi: Gina Makomar Nijeriya Ta Hanyar Tallafa Wa Kananan Kamfanoni
Wanda Da Ya Fi Tasiri A Kafofin Sada Zumunta Na Shekarar 2025
13. Domin sauya rikici zuwa hadin kai, da tashin hankali zuwa ci gaba mai ma’ana da kirkirar ayyukan yi, samar da zaman lafiya da sabunta zamantakewa, al’adu da tattalin arzikin Neja Delta da zuba jari a ilimi, kiwon lafiya, muhalli da karfafa ci gaba, an zabi Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo) a matsayin mafi tasiri a Kafofin Sada Zumunta na 2025.
Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba
Gwarzuwar Hukumar Gwamnati Ta Shekarar 2025
14. Domin fadada iyakokin aiwatar da doka a Nijeriya tare da dawo da fiye da naira biliyan 10 ga masu amfani da kayayyaki tare da kalubalantar rashin adalci na kamfanoni da kafa sabbin ka’idoji kula da kasuwanci ta kafafen sadarwar zamani da tabbatar da adalci da shugabanci na na gari — Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani da Kayayyaki ta Kasa (FCCPC), ita ce Gwarzuwar Hukumar Gwamnati ta Shekarar 2025.
Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani Da Kaya (Fccpc): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa
SkalesShi Ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025
15. Sakamakon tasirin da ya dade yana yi a fannin waka a Nijeriya da kasashen waje. Shahararriyar wakarsa “Shake Body”, wacce ta kai ga samun miliyoyin masu sauraro a Spotify da kuma kwarewarsa a fannin fasahar hada al’umma daban-daban. SKALES ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025.
Kanyenyachukwu Tagbo Okeke Shi Ne Gwarzon Mai Zane Na Shekarar 2025
16. Saboda sanya Nijeriya a taswira ta duniya tare da Guinness World Record (GWR) na Mafi Girman Zanen Canbas da mutum daya ya yi a wannan shekara, da kuma wayar da kan jama’a kan cutar autism a Nijerriya, tare da amfani da fasaha wajen karfafa hadin kai da ilimi ga mutane masu kwarewa daban-daban, Kanyenyachukwu (wanda aka fi sani da Kanye) Tagbo-Okeke shi ne Gwarzon Mai Zane na Shekara 2025.
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025
17. Saboda jagorantar Super Falcons zuwa nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10, wanda ya kara musu tasiri; da nuna kwarewa a dabaru da shugabanci da dawo da aminci a kwallon kafar Nijeriya da kuma karfafa sabon karni na masu horar da kwallo a Afirka, Justine Madugu shi ne gwarzon mai koyar da wasanni na Shekarar 2025.
Justine Madugu: Mai Dabaru Dawo Da Darajar Kwallon Kafa A Nijeriya
Dabid Adeyemi Shi Ne Gwarzon Matashi Na Shekara 2025
18. Dangane da habaka kirkira, tausayi da kwarewa ta hanyar kirkirar manhajar AI wacce ke sauya yadda dalibai masu nakasar gani ke samun ilimi a Nijeriya da wajenta, Dabid Adeyemi shi ne Gwarzon Matashi na Shekarar 2025.
Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025
19. Domin ganin yadda ya sauya akalar samar da kiwon lafiya cikin tausayi da soyayya ga mabukata tare da yi wa mutane fiye 2,600 tiyata kyauta a sassan kasar nan. Dr Seidu Adebayo Bello shi ne Gwarzon Ma’aikacin Kiwon Lafiya na shekarar 2025.
Dr Seidu Adebayo Bello: Ya Dawo Da Fata Ga Al’umma
Misis Mabel Ijeoma Duaka Shi Ne Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025
20. Duk da ayyukan ta’addanci na Boko Haram, yayin da al’umma musamman baki ke gudu daga yankuna da dama na Jihar Borno, ta gwammace ta zauna a karamar hukumar Mafa domin ci gaba da bayar da kulawa ga wadanda suka jikkata na tsawon shekara 21. Mrs Mabel Ijeoma Duaka ce Gwarzuwar Ma’akaciyar jinya ta shekarar 2025
Bankin Probidus Ne Gwarzon Banki Na Shekarar 2025
21. Saboda kasancewa kan gaba wajen zamanantar da harkokin Banki a Nijeriya da kuma karfafa wa manya da kananan masa’na’antu tare da zama a kan gaba wajen daukaka darajar aikin Banki a Nijeriya, Bankin Probidus ne Gwarzon bankinmu na shekarar 2025.
Gwarzuwar Matashiya ‘Yar Makaranta Ta Shekarar 2025
22. Domin nasarar da ta samu wajen sanya sunan Nijeriya a fagen ilimi a duniya da jajircewa, hazaka da bayar da shawarwari don zaburar da sabbin dalibai don rungumar harshe Turanci da tabbatar da nasara na iya tasowa daga kowane bangare. An bai wa Nafisa Abdullahi Aminu lambar yabo ta Gwarzuwar Matashiyar 2025.
Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Daukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya
Hukumar NASENI Ne Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025
23. Domin yadda ta jagoranci ci gaban masana’antu, samar da makamashi, da fasahohin da suka dace da yanayin da ke rage fitar da iskar carbon mai guba da inganta hanyoyin samar da wutar lantarki mai tsabta; karfafa masu kirkire-kirkire na cikin gida, samar da dabarun tattalin arzikin mai dorewa, da habaka dogaro da kai a Nijeriya ta hanyar bincike da kula da muhalli, Hukumar NASENI ce Gwarzuwar Hukumar da ta fi tasiri wajen kare muhalli a shekarar 2025.
Gwarzon Kamfanin Fasahar Kudade Na Shekarar 2025
24. Don kawo sauyi a harkokin kudade ta hanyar fasahar zamani da suka hada da kirkira da gaskiya wajen karfafa miliyoyin ‘yan Nijeriya, kanana da matsakaitan kamfanoni (MSME) ta hanyar amfani da wayar hannu, don kawo karshen matsalolin kudade ta hanyar fasahar zamani, OPay Nigeria ya amsa sunansa na zama gwarzon kamfanin fasahar harkokin kudade na shekarar 2025.
OPay Nigeria: Tabbatar Da ‘Yancin Hada-hadar Kudi
Kamfanin GEIL: Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025
25. Domin jagorantar bunkasawa da gudanar da tashar fitar mai na farko a Nijeriya fiye da shekaru 50, Kamfanin GEIL shi ne Gwarzon Shekarar 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025
26. Domin habaka samar da ruwan sha mai inganci da arha, dandano da wayar da kan ‘yan kasa kan amfani da tsaftataccen ruwa, kamfanin Nestlé Pure Life Nigeria Plc shi ne gwarzon samar da kaya a shekarar 2025.
Kamfanin Nestlé Pure Life: Tsarinsa Da Manufa
Kamfanin Trade Modernisation Project: Gwarzon Kamfani Na Shekarar 2025
27. Domin sauya tsarin kasuwancin Nijeriya ta hanyar fasahar zamani da inganci, sarrafa ayyuka, kara habaka samun kudaden shiga da saukaka gudanar da kasuwanci, bunkasa hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da karfafa gasa, Kamfanin Trade Modernisation Project (TMP) shi ne gwarzon Kamfanin shekarar 2025.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Gwarzon Ma aikacin a matsayin Gwarzon shi ne Gwarzon Ma Gwarzuwar Hukumar Gwarzon Kamfanin ta shekarar 2025 na shekarar 2025 gwarzon Kamfanin ta Shekarar 2025 Ta Shekarar 2025 Na Shekarar 2025 Nijeriya da kuma na Shekarar 2025 Gwarzon Gwamnan a shekarar 2025 shi ne gwarzon a Nijeriya da Gwarzuwar Ma zaman lafiya Nijeriya Ta gwarzon mai Nijeriya ta more rayuwa Gwarzon Mai
এছাড়াও পড়ুন:
Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya nemi sabbin hafsoshin tsaron ƙasar su zage damtse domin magance duk wata barazanar tsaro da ake fuskanta a halin yanzu da ma wadda ka iya kunnowa nan gaba.
Shugaban ya gargadi sabbin hafsoshin tsaron cewa ’yan Nijeriya sakamako kawai suke buƙata, ba uzuri ba, saboda haka dole ne su cika aikin da aka ɗora musu.
Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026 Ƙwallo ta kashe ɗan wasan CricketTinubu ya bayyana hakan ne bayan bikin ƙara wa sabbin hafsoshin tsaron da shugabannin rundunonin soji girma da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa yau Alhamis a Abuja.
A cewarsa, “Barazanar tsaro na ƙara sauyawa a kodayaushe, kuma abin da ya fi damun gwamnatinmu shi ne ɓullar sababbin ƙungiyoyin ’yan bindiga a Arewa ta Tsakiya, da Arewa maso Yamma, da wasu sassa a Kudanci.”
A ranar Laraba ce Majalisar Dattawa da ta Wakilai suka amince da naɗin Laftanar Janar Olufemi Oluyede a matsayin Babban Hafsan Tsaro; Manjo Janar Waidi Shaibu a matsayin Hafsan Sojan Ƙasa; Rear Admiral Idi Abbas Hafsan Sojan Ruwa; Air Marshall Kennedy Aneke Hafsan Sojan Sama; da Manjo Janar Emmanuel Undiendeye a matsayin Shugaban Tattara Bayanai na Soja.
“Ba zai yiwu mu ƙyale wannan sabuwar barazanar ta ci gaba ba. Dole ne mu ɗauki mataki da wuri. Mu sare kan macijin.
“’Yan Najeriya suna sa rana ganin sakamako, saboda haka babu wani uzuri da za su karɓa. Ina kuma kira da ku kasance masu dabaru da hangen nesa da kuma jarumta.
“Mu kasance mun tari hanzarin duk waɗanda ke neman tayar da zaune tsaye a ƙasarmu,” in ji Tinubu.
Yayin bikin, an ƙara wa Olufemi Oluyede muƙami zuwa Janar, Waidi Shaibu zuwa Laftanar Janar, Idi Abbas zuwa Vice Admiral, da Kevin Aneke zuwa Air Vice marshall, da kuma Emmanuel Undiendeye zuwa Laftanar Janar.