An yi garkuwa da tsohon Shugaban SUBEB na Jihar Neja
Published: 30th, September 2025 GMT
Tsohon Shugaban Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Neja (SUBEB), Alhaji Alhassan Bawa Niworo, ya shiga hannun ’yan bindiga.
An yi garkuwa da shi tare da wasu fasinjoji da dama a yammacin Litinin, 29 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 4 na yamma, tsakanin ƙauyukan Felegi da Ibi a kan hanyar Mokwa zuwa New Bussa a Ƙaramar Hukumar Borgu.
Wata majiya ta ce Niworo tare da wasu ciki har da wani lauya, Barista Ahmad, na kan hanyarsu zuwa Minna ne lokacin da ’yan bindigar suka tare hanyar, suka kuma yi awon gaba da su cikin daji.
Wasu daga cikin waɗanda aka sace ’yan kasuwa ne da suka fito daga kasuwar mako ta New Bussa.
Abin da ya faru a zaman sulhun PENGASSAN da Matatar Ɗangote Jama’ar gari sun kama ’yan bindiga 3 a Kastina Manoma na tserewaAl’ummar karkara a ƙananan hukumomin Mariga, Magama, Kontagora, Mashegu, Borgu da Rijau a yankin Neja ta Arewa maso Yamma na ci gaba da barin gidajensu saboda hare-haren da suka ƙaru a kwanaki biyar da suka wuce.
Da sanyin safiyar Talata, ’yan bindiga fiye da 200 sun kutsa garin Ibeto a da aka Magama, abin da ya tilasta mazauna su tsere.
A wani bidiyo da wani mazaunin ya yada, an nuna mata da yara suke gudun hijira cikin duhu da fitilun hannu.
Wata majiya ta ce: “Da tsakr dare suka kai hari a Dogon-Daji, Ugulu, Maira, Atabo da Ibeto. Sun kuma shiga Lioji kafin su dawo su kai farmaki a Maira, Ugulu, Atabo da Ibeto. A Atabo, sun yi awon gaba da mutane da dama bayan sun kasa samun shanu da za su sace.”
Majiyar ta ƙara da cewa, “Mazauna Ibeto sun tsere kafin daga bisani ’yan bindigar su mamaye kauyen. An ji harbe-harben bindiga amma ba a tabbatar da asarar rayuka ba.”
Wani mazaunin ya bayyana cewa, “Sun shiga Magama da safe kafin su isa Yangale inda suka yi garkuwa da mutane huɗu. Muna cikin daji da mata da yara. Don Allah ku taya mu da addu’a, muna bukatar taimako.”
A ranar Asabar, sama da ’yan bindiga 100 sun kutsa garin Talle a yankin Kulho na Karamar Hukumar Mashegu.
Mazauna sun ce maharan sun iso kauyen da misalin ƙarfe 2 na rana, suka umarci masu shaguna su rufe. Sun kuma toshe duk hanyoyin shiga da fita daga garin, sai kaɗan da suka yi nasarar guduwa.
Hakazalika, mazauna Ragada da wasu kauyuka a Mariga sun bar gidajensu tun ranar Lahadi saboda motsin ’yan bindiga a yankin.
Wani daga cikinsu ya ce, “Mun kwana a kan duwatsu duk da ruwan sama, yayin da muna kallo ’yan bindiga suna dafa abinci a gidajenmu.”
A ranar Asabar da rana kuma, an yi garkuwa da matafiya da dama a kan hanyar Kontagora–Rijau.
Martanin ’yan sandaKakakin rundunar ’yan sanda ta Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da harin da aka kai a hanyar Ibbi–New Bussa.
Ya ce wani ɗan sanda ya ji rauni, sannan motar sintirin ’yan sanda ta lalace yayin musayar wuta da ’yan bindigar.
Ya ce: “A ranar 29 ga Satumba, 2025, da ƙarfe 11:30 na safe, wasu ’yan bindiga suka kai hari a wurin sintirin ’yan sanda a kan hanyar Ibbi–Bussa.
“Jami’an sintirin sun yi nasarar mayar da martani, amma motar sintirin ta samu rauni, sannan ɗaya daga cikin ’yan sanda ya ji harbin bindiga kuma aka kai shi asibiti
Ya ƙara da cewa: “Abin takaici, ’yan bindigar da suka tsere daga wurin sun toshe hanyar a gaba, suka yi awon gaba da fasinjoji daga akalla motoci uku.
“Rundunar ta tura ƙarin jami’an sintiri tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro da sa-kai domin bin sawun masu garkuwa da nufin ceto mutanen da aka sace da kuma kama maharan.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Garkuwa yi garkuwa da yan bindigar a kan hanyar yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Ɓangaren Shari’a a Nijeriya, yana da alhakin bayyana dokoki, kare kundin tsarin mulki, da kuma tabbatar da adalci. An tsara tsarin shari’a a karkashin jagorancin Kotun Ƙoli inda Alƙalin Alƙalan Nijeriya (CJN) ke kula da ita, sannan Kotun Ɗaukaka Ƙara da Manyan Kotuna a matakin jiha da tarayya.
Daga cikin manyan haƙƙoƙin da suka rataya akan ɓangaren Shari’a, akwai fassara kundin tsarin mulki da dokoki don amfani da su a shari’o’i. Sulhunta masu saɓani da kare haƙƙin ‘yan ƙasa da kuma tabbatar da cewa, sauran sassan gwamnati suna aiki a cikin iyakokin kundin tsarin mulki.
Amma, mu tambayi kanmu, wai me ke faruwa a ɓangaren Shari’a, ake samun hukuncin Shari’a ɗaya masu karo da juna?
An samu ruɗani a Kano a ranar Talata, 29 ga Mayu, 2024 bayan wani umarnin kotu guda biyu masu karo da juna game da taƙaddamar da ta taso kan sarautar Masarautar Kano tsakanin Sarki Muhammadu Sanusi na II da Aminu Ado Bayero, sarkin da aka sauke.
Yayin da Mai Shari’a S. Amobeda na Babbar Kotun Tarayya, Kano, ya umarci Sufeto Janar na ‘Yansanda, Kayode Egbetokun, da Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kano, Hussain Gumel, da su tabbatar da cewa, an bai wa Aminu Ado Bayero dukkan haƙƙoƙin gata da ake bai wa sarakuna, nan take kuma, Mai Shari’a Amina Aliyu ta Babbar Kotun Jihar Kano ta hana ‘yansanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da Sojojin Nijeriya korar Muhammadu Sanusi na II, Sarkin Kano da aka dawo da shi kan kujerar sarautar.
Taƙaddamar dai ta fara ne a lokacin da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauke Bayero daga kan sarautar Masarautar Kano, tare da wasu Sarakuna huɗu na Rano, Bichi, Karaye da Gaya inda kuma ya mayar da Lamido Sanusi a matsayin Sarki bayan soke dokar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya yi amfani da ita wajen sauke shi daga kujerar mulki a shekarar 2020.
Da yake magana kan halin da ake ciki a Kano, wani lauya mazaunin Abuja, Kennedy Khanoba, yayin da yake tattaunawa da Jaridar PUNCH ya roƙi Shugaba Bola Tinubu da ya bar doka ta yi aiki, a ajiye maganar siyasa a gefe, yanzu doka tana hannun gwamnan jihar.
Har ila yau, Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta nuna rashin jin daɗi game da hukunce-hukuncen da ke karo da juna daga kotuna.
Ƙungiyar lauyoyin ta yi wannan kira ne yayin da take yi wa ‘yan jarida bayani kafin Makon Shari’a na 2025, inda ta kuma yi kira da a yi gyare-gyare don daidaita shari’o’in kafin zaɓen dake tafe a ƙasar.
Sai dai, shugaban na NBA reshen Akure, ya yi karin haske da cewa, “wani lokacin, yanke hukuncin masu karo da juna, suna tasowa ne daga bambance-bambancen ra’ayoyin alkalai” kuma ya amince cewa Majalisar Shari’a ta Ƙasa (NJC) tana ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yanayi. Yayin da wasu masu ruwa da tsaki a ɓangaren Shari’a ke zargin ke zargin ɓangaren zartarwa da tsoma baki a Shari’o’in da suke da wani ra’ayi na musamman akai.
To, ko meye ke haifar da wannan hukunce-hukuncen masu bugu da juna?
ShareTweetSendShare MASU ALAKA