Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4
Published: 25th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya rattaba hannu kan wasu sabbin dokoki guda huɗu da suka kafa muhimman hukumomi domin ƙarfafa tsarin gudanarwa na jihar da kuma haɓaka ci gaba mai ɗorewa.
Waɗannan dokokin za su samar da Hukumar Kare Hakkokin Jama’a ta Jihar Kano (KASPA), Hukumar Kula da Tallace-tallace da Rubuce-rubuce ta Jihar Kano (KASIAA), Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa da Zamani ta Jihar Kano (KASITDA), da kuma Hukumar Bunƙasa Ƙananan Kasuwanci da Matsakaita ta Jihar Kano (KASMEDA).
Gwamna Abba, ta bakin mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana muhimmancin waɗannan dokokin wajen ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire, tallafa wa ƙananan kasuwanci, tsara tallace-tallace, da inganta kare hakkin jama’a da samar da ayyuka.
Ya jaddada cewa waɗannan hukumomi za su taka muhimmiyar rawa wajen samar da ayyukan yi, jawo jari, da kuma aiwatar da tsare-tsaren gwamnati yadda ya kamata, wanda ya nuna hangen nesansa na sanar da Kano ta zamani da bunƙasa tattalin arziki.
Ƙarin ’yan Najeriya za su shiga talauci nan da 2027 — Bankin Duniya ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a NasarawaGwamnan ya yi gargaɗi game da keta waɗannan sabbin dokokin, yana mai cewa za a hukunta duk wanda ya karya su da tsauraran matakai domin tabbatar da bin doka da oda.
Kafa waɗannan hukumomi ya nuna ƙoƙarin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ci gaba da gyara cibiyoyin gwamnati, inganta gudanarwa, da kuma sanya Kano a matsayin cibiyar da ta fi fice a fannin ƙirƙire-ƙirƙire, kasuwanci, da ci-gaba mai ɗorewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Tattalin Arziki ta Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano
Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya naɗa babban ɗan uwansa, Alhaji Sanusi Ado Bayero, a matsayin Galadiman Kano, bayan rasuwar Abbas Sanusi.
A gefe guda kuma, Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, wanda ke ta ƙaddamar kan sarautar Kano da Aminu Ado Bayero a gaba kotu, ya naɗa Mannir Sanusi a matsayin Galadiman Kano.
Wannan lamari na nuni da cewa rikicin Sarautar Kano ya ɗauki sabon salo, inda kowanne daga cikin ɓangarori biyun ya naɗa nasa Galadiman Kano, inda masu riƙe da sarautun biyu za su gudanar da ayyukansu daban-daban.
A cikin wasiƙar da ke ɗauke da wannan sanarwar, wadda Alhaji Awaisu Abbas Sanusi, babban jami’in gudanarwa na Majalisar Masarautar Kano ya sanya hannu, naɗin Sanusi Ado Bayero ya biyo bayan taron majalisar da Sarki Aminu ya jagoranta a ranar Laraba, 16 ga Afrilu, 2025.
Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”A baya an naɗa Sanusi a matsayin Chiroman Kano, dan Majalisar Masarautar Kano, kuma Hakimin Gwale a zamanin mahaifinsa Sarki Ado Bayero.
Bayan rasuwar mahaifin nasa a shekarar 2014, a matsayinsa na babban ɗa kuma magaji, an ɗauka cewa Sanusi Ado ne wanda ya cancanci ya gaje shi, War wasu rahotanni na farko sun sanar da shi a matsayin Sarki.
Sai dai, a ranar 8 ga Yuni, 2014, aka naɗa ɗan ɗan uwansa, Sanusi Lamido Sanusi, a matsayin Sarkin Kano. A sakamakon haka, Sanusi Ado ya ƙi yin mubaya’a a gare shi kuma, don nuna rashin amincewa, kuma ya yanke shawarar barin Kano.
Bayan raba Masarautar Kano, da cire Sarki Sanusi II, da kuma naɗin ƙanensa, Aminu Ado Bayero, a matsayin Sarki na 15 a watan Yulin 2020, an mayar da Sanusi Ado Bayero kan matsyinsa a Majalisar Masarautar Kano kuma aka ba shi sarautar Wamban Kano.
Tarihin Sanusi Ado BayeroSanusi kammala digirinsana farko a fannin shari’a a shekarar 1983 kuma an rantsar da shi a matsayin lafiya a shekarar 1984.
Tsohon ma’aikacin Gwamnatin Jihar Kano ne inda ya yi aiki daga 1985 zuwa 2015, har ya kai matsayi mafi girma na Babban Sakataren.
Daga baya aka naɗa shi a matsayin Manajan Daraktan Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya, muƙamin da ya riƙe har zuwa lokacin da aka cire shi a watan Agustan 2015.