Jigawa Za Noma Rabin Shinkafa Da Ake Amfani Da Ita A Nigeria Nan Da 2030
Published: 25th, April 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya ce gwamnatinsa na shirin bayar da gudunmawar kashi 50 na shinkafar da Najeriya ke bukata nan da shekara ta 2030.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar tawagar hukumar tattara kudaden shiga da kasafi (RMAFC) karkashin jagorancin shugaban kwamitin inganta kasafin kudi da kasafin kudi, Ambasada Desmond Akawor, yayin ziyarar ban girma da suka kai a gidan gwamnati dake Dutse.
Ya bayyana cewa, suna noman shinkafa sau biyu a shekara, inda ya nuna cewa, a shekarar 2024 kadai, sun noma sama da hekta 200,000 na shinkafa.
Ya yi nuni da cewa, a bana, suna son noma sama da hekta 250,000 wanda a shekarar 2030, burinsu ya kai kadada 500,000.
Malam Umar Namadi ya ce, a irin takun da suke tafiya za su cimma hakan cikin sauki.
“Babban burinmu shi ne mu ba da gudummawar metric ton miliyan 3.6 na shinkafa kowace shekara don noman shinkafar Najeriya – wanda ke wakiltar kusan kashi 50% na abin da al’ummar kasar ke bukata. Muna da kasa, jama’a, da siyasa don ganin hakan ta tabbata.”
Gwamna Namadi ya ce har yanzu noma shi ne jigon tattalin arzikin Jigawa, inda kusan kashi 85% na al’ummarta ke tsunduma a wannan fanni, inda ya ce gwamnatinsa ta samu nasarorin tarihi a harkar noman rani a yankunan da ba su da yawa a jihar.
Dangane da tallafin albarkatun kasa, gwamnan ya bayyana irin ma’adinan da ba a yi amfani da su a Jigawa ba, ciki har da mai, amma ya bayyana yadda gwamnati ke taka-tsantsan wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.
Tun da farko, shugaban tawagar RMAFC ya shaida wa gwamnan cewa ziyarar na daga cikin ayyukan da kwamitin ya ba su na tantance ayyukan da suka dace a matakin jihohi ta hanyar ware kudaden shiga na musamman na kasa da kashi 1.68 cikin 100 da nufin karkatar da tattalin arzikin Najeriya, tare da mai da hankali kan noma, yawon bude ido, da ma’adanai masu inganci.
Ya ci gaba da cewa kwamitin ya yaba da yadda aka fara gabatar da jawabai da ziyarce-ziyarcen wuraren da aka fara yi, musamman irin abubuwan da suka shafi albarkatun kasa a jihar, kuma za su ci gaba da duba harkokin noma tare da baiwa gwamnan tabbacin tantance gaskiya.
Ya kuma jaddada muhimmancin amfani da albarkatun kasa domin bunkasar tattalin arziki.
KARSHE/USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
Semenyo ma ya taka rawar gani saboda kwallo biyun da ya ci a wasan karshe sun sa ya ci wa kungiyarsa Bournemouth kwallo 11 kenan a karonfarko.
Danwasan Najeriya Aled Iwobi ya fi abokan wasansa kokari a Fulham da kwallayensa tara da ya ci da kuma taimakawa wajen cin shida, sannan ya dan dara Amad Diallo na Manchester United (wanda ya ci takwas kuma ya bayar aka ci shida). Amma Iwobi ya fi shi buga wasanni saboda Diallo ya yi jinyar wajan watanni uku a kakar da ta gabata. Iwobi ne dai kan gaba wajen kirkirar damarmaki (59) da kuma bayar da cikakken fasin (508) a cikin bangaren abokan hamayya, inda shi kuma.
Thomas Partey na Ghana ya fi yawan tura cikakkun fasin (1,631). Shi kuwa Idrissa Gana Gueye ya nuna bajintarsa ne wajen taimka wa Eberton samun damar ci gaba da zama a gasar. Dan Senegal din mai shekara 35 ya cim ma mafi girman bajintar dakatar da abokan hamayya sau 133 kuma ya dauke kwallo daga abokin hamayya sau 221, inda ya zarta kowane dan kwallo daga nahiyar Afrka.
Aaron Wan-Bissaka, shi ne ya fi kowa tare kwallo (66) kuma ya fi yawan yin yanka (64) a ‘yanwasan bayan Premier League – hakan ya sa magoya bayan West Ham suka zabe shi gwarzonsu a bana. Dan Ajeriya Rayan Ait-Nouri, wanda ya koma kungiyar Manchester City a wannan watan ya nuna bajintar kai hari duk da matsayinsa na danwasan baya ta gefe, inda ya ci wa tsohuwar kungiyarsa ta Wolbes kwallo hudu kuma ya bayar aka ci bakwai.
Dan wasa Ola Aina ya taka rawa mafi kyau a tarihi sana’arsa a Nothingham Fores, inda ya dinga kwalo daga ƙafar abokan hamayya sau 190 – mafi yawa kenan da wani danwasan baya ya taba yi. Dan Najeriyar mai buga baya a bangaren dama ya cire kwallo daga kan layin shiga raga sau uku, wanda ‘yanwasa shida ne kawai suka iya yin irin wannan bajintar cikinsu kuma har da Iliman Ndiaye na Senegal.
Calbin Bassey na Najeriya ya taba kwallo sau 2,536 a Fulham – fiye da kowane dankwallon Afirka kenan a gasar – da cikakken fasin 1,926 da ya bayar, da tsige kwallo sau 113, da hana kwallo wucewa sau 17. A gefe guda kuma, Noussair Mazraoui ya tare abokan hamayya sau 115 da kuma dauke kwallo sau 216 daga abokin hamayya a Manchester United.
Andre Onana, mai tsaron raga dan Afirka tilo a Premier League, ya fuskanci kalubale mai girma a kakar bana yayin da Manchester United ta shiga tasku mafi muni cikin shekara 50. Mai tsaron ragar na Kamaru ya buga wasa tara ba tare da an zira masa kwallo a raga ba, amma kuma an ci shi kwallo 44 cikin wasa 25. Hana kwallo shiga raga sau 90 da ya yi shi ne karo na 12 kuma mafiya yawa,
inda adadin ya zama kashi 66 cikin 100 kuma na 15 kenan a tsakanin masu tsaron da suka buga wasa 10 ko fiye da haka. Danwasan mai shekara 29 ya yi kuskure uku da suka jawo zira masa kwallo a raga – ‘yanwasa uku ne kawai suka yi fiye da hakan.
Tarihi mara amfani
Danwasan da ya fi kowa yin keta a kakar Premier ta 2024-25 shi ne, Semenyo na Bournemouth, wanda aka busa wa laifi sau 73. Adadin ya zarta na kowane dan wasan Afirka. Samy Morsy na Ipswich Town da kasar Masar, shi ne ya fi kowanne dan Afirka samun katin gargadi (10), sai Gueye da Semenyo da ke da 9 kowanne. An kwace kwallo daga kafar Mohammed Kudus na Ghana da West Ham sau 93, sannan ya buga kwallon da ta daki turke sau shida. Salah da Jackson da Palmer ne kawai suka zarta shi.
Danwasan gaban Chelsea da Senegal Jackson ya yi satar gida fiye da kowa har sau 23. Chris Wood, da Dominic Calbert-Lewin, da Jamie Bardy ne kadai suka kara shi.
Shi kuma dan wasa Taiwo Awoniyi ya fi kowanne dan kwallon Afirka shiga wasa daga baya a Forest, inda Jack Taylor na Ipswich ne kawai ya dara shi zama a bencin. Wasa 23 cikin 26 da dan Najeriyar ya buga ya shiga ne bayan fara wasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp