HausaTv:
2025-11-02@21:15:25 GMT

 WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani

Published: 23rd, April 2025 GMT

Hukumar lafiya ta duniya  (W.H.O ) ta sanar da cewa rashin magani da na’urorin wanke koda a Gaza, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 400 masu fama da wannan cutar.

Hukumar lafiyar ta duniya ( w.h.o) ta kuma yi ishara da yadda ‘yan mamaya su ka lalata bangarorin da suke kula da cutuka na musamman a cikin asibitoci.

Ita ma hukumar lafiya ta Gaza ta bayyana cewa; masu fama da cutar koda a yankin suna fama da matsaloli na rashin Magani, kuma daruruwa daga cikinsu sun mutu saboda hakan.

Haka nan kuma ta  yi ishara da yadda mutane 400 daga cikinsu su ka rasu, da hakan yake nufin kaso 40% na adadin masu wannan cutar.

A gefe daya, ma’aikatar kiwon lafiyar ta Falasdinu ta yi tir da yadda ‘yan mamaya su ka kai wa asibitin “Durrah” na yara hari a gabashin birnin Gaza.

Haka nan kuma hukumar kiwon lafiyar ta Gaza, ta tabbatar da cewa hare-haren da ‘yan mamayar su ka kai wa dakin da yake kula da marasa lafiya na musamman a cikin asibitin kananan yaran, da kuma tashar samar da wutar lantarki a cikin asibitin.

Sanarwar hukumar lafiya ta Gaza ta ce, baya ga hana shigar da abinci da magani da ‘yan mamayar suke yi, suna kuma hana Falasdinawa ci gaba da rayuwa. Ita kuwa hukumar agaji ta “Red-Crecent” ta bayyana cewa; ‘Yan mamaya sun tafka laifukan yaki da su ka hada da kashe masu aikin agaji a cikin watan Maris.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hukumar lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

A 2022, kasashe shida ne suka daina yanke hukuncin kisa, ko dai gaba daya ko kuma wani bangare.

Hudu daga cikinsu; Kazakhstan, Papua New Guinea, Saliyo, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sun jingine shi kwatakwata.

Ekuatorial Guinea da Zambia sun ce za a rika amfani da shi ne kawai kan laifuka mafiya kololuwar muni.

A watan Afrilun 2023, majalisar dokokin Malaysia ta kada kuri’ar daina amfani da shi a matsayin tilas kan laifuka 11, ciki har da kisa da kuma ta’addanci.

Majalisar dokokin Ghana ma ta kada kuri’ar soke hukuncin kisa a watan Yulin 2023.

 

Wadanne kasashe ne suka fi yanke hukuncin kisa?

Kasashe 20 ne suka zartar da hukunbcin kisa a 2022, idan aka kwatanta da 18 da suka yi hakan a 2021.

Kungiyar kare hakki ta Amnesty International ta ce jimillar mutum 1,518 aka zartar wa hukuncin kisa a duniya, inda aka samu karin kashi 32 cikin 100. Sai dai ta ce hakikanin adadin ya zarta haka sosai saboda yadda kasashe ke boye batun.

Bayan China, Amnesty ta ce kasashen da suka fi kashe mutane a 2024 su ne Iran (972), da Saudiyya (345), da kuma Iraki (63). Su ne suka zartar da kashi 91 cikin 100 na duka kasashen duniya.

Ana yi wa China kallon kasar da ta zarta kowacce aiwatar da hukuncin kisa a duniya, amma ba a sanin hakikanin adadin mutanen, saboda gwamnati ba ta bayyana su.

Kasashen Koriya ta Arewa da Bietnam ma na amfani da hukuncin kisa sosai amma ba su bayyanawa a hukumance.

Amnesty ta ce ta samu rahoton zartar da hukuncin kisa a bainar jama’a akalla sau uku a 2022 a Iran.

Ta ce Iran din ta kashe akalla mutum biyar saboda laifukan da suka aikata a lokacin da suke kasa da shekara 18 da haihuwa.

Saudiyya ta kashe mutane mafiya yawa a duniya a 2022 cikin shekara 30.

Kasashe biyar; Bahrain, Comoros, Laos, Nijar, Koriya ta Kudu – su ne suka yanke wa mutane hukuncin kisa a 2022 bayan sun shafe tsawon lokaci ba su yi amfani da shi ba.

Duk da cewa adadin na raguwa a Amurka, amma ya karu a 2021, amma duk da haka ya yi kasa sosai idan aka kwatanta da shekarar 1999.

 

Mutum nawa aka kashe saboda safarar miyagun kwayoyi?

Amnesty International ta ce sama da kashi 40 cikin 100 na mutanen da aka zartar wa hukuncin kisa a 2024 saboda laifukan ta’ammali da miyagun kwayoyi ne.

A 2022, an kashe mutum 325 saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi. Kasashen da suka aikata hakan su ne:Iran 255 Saudiyya – 57 – Singapore – 11

A 2023, Singapore ta zartar da hukuncin kisa kan mace ta farko cikin shekara 20. A 2018 aka kama Saridewi Djaman da laifin safarar hodar ibilis.

 

Ta yaya kasashe ke zartar da hukuncin kisa?

Saudiyya ce kadai ta zayyana fille kai a matsayin hanyar aiwatar da hukuncin kisa a 2022.

Sauran hanyoyin sun hada da rataya, da allura mai guba, da kuma harbi da bindiga.

A watan Janairun 2024 jihar Alabama ta Amurka ta zartar wa wani mai laifin kisa Kenneth Smith hukuncin kisa ta hanyar amfani da iskar nitrogen gas.

Ya zama mutum na farko a duniya da aka zartar wa hukuncin ta irin wannan hanyar, a cewar cibiyar Death Penalty Information Center da ke Amurka.

Lauyoyin Mista Smiths sun ce salon da ba a taba gwadawa ba kafinsa “rashin imani ne”.

Alabama da wasu jihohin Amurka biyu ne suka amince da amfani da iskar gas din saboda kwayoyin da ake amfani da su wajen yi wa mutum allura mai guba ba sa samuwa cikin sauki.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa