Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
Published: 23rd, April 2025 GMT
Ƙungiyar shugabannin majalisun jihohin Nijeriya ta yi tur da matsalolin tsaron da suka addabi jihohin Filato, Borno, Binuwai, Neja, da kuma Kwara a baya-bayan nan.
Ƙungiyar ta buƙaci gwamnatocin jihohi da na tarayya da su ɗauki matakan gaggawa domin daƙile bala’in da jihohin a kwanan nan suka tsinci kansu a ciki.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a Ibadan da ke Oyo mai dauke da sa hannun shugabanta, Adebo Ogundoyin.
Ya bayyana cewa kashe-kashen dubunnan al’ummar da ba su ji ba, ba su gani ba ya janyo musu asarar gidajensu, da dukiyoyinsu, yana haifar musu da tashin hankali.
“Mun kaɗu ƙwarai da yadda matsalar tsaro ke ƙara ƙamari a Nijeriya, da kuma rashin tabbas da ke biyo bayan kashe-kashen.
“Lokacin yin Allah-wadai ya wuce, yanzu matakin gaggawa ya dace gwamnatocin dukkanin matakai su ɗauka domin kawo karshen masifar nan.
“Mun san cewa tsaron kasa na hannun gwamnatin Tarayya ne, amma mu sani gwamnatin kowanne mataki na da alhakin tsaro da walwalar jama’arta, musamman gwamnonin jihohi.
“Bai dace aikinku ya tsaya a yin tituna da tarukan bukukuwa ba. Gwamnatin gaskiya ita ce wacce ta kafu akan kare rayukan al’umma, tabbatar da doka da oda, da kuma raba su da wahala.” In ji shi.
Daga nan ya yi kira ga gwamnatocin jihohin da su taimaka wa yunƙurin gwamnatin tarayya a ɓangaren tsaro ta hanyar samarwa da tilasta bin dokoki da sauran tsare-tsare a matakin unguwanni.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Binuwai Kwara matsalar tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing
Da safiyar yau 17 ga watan Satumba, aka bude dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan karo na 12 da zai dauki kwanaki 3, daga raneku 17 zuwa 19 ga wannan nan, bisa jigon “daukaka tsarin duniya da inganta neman ci gaba cikin lumana”, a nan birnin Beijing.
Tawagogi sama da 100 na gwamnatocin kasashe daban-daban da yankuna da wakilan kungiyoyin kasa da kasa ne ke halartar taron, inda yawan masu rajista ya wuce 1,800.
Da safiyar yau, taron ya shirya tarukan tattaunawa guda 6 bisa jigon “ma’anar cimma nasarar yakin duniya na kin tafarkin murdiyya” da “madaidaitan hanyoyi da manyan kasashe za su bi na yin mu’ammala”, da “hanyoyin warware rikice-rikicen shiyya-shiyya”, da “cika shekaru 80 da kafuwar MDD: samun ci gaba cikin sauye-sauye”, da “amfani da sarrafa sabbin fasahohi”, da kuma “kirkire-kirkire a bangaren kimiyya da fasaha da sauye-sauyen yanayin yaki”. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp