Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
Published: 23rd, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: China da Rasha abokan hulda ne na tushe ga Iran bisa kyakkyawan tsari
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana kasashen China da Rasha a matsayin abokan huldar na tsari a kan tubalin manyan tsare-tsare ga Iran, kuma ya dace kasashen uku su ci gaba da tuntubar juna a fannoni daban daban.
A yayin da ya isa birnin Beijing, yayin da yake amsa tambaya game da makasudin ziyararsa a kasar China a jajibirin shawarwarin da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, Araqchi ya bayyana cewa: Kasashen China da Rasha abokan hulda ne na kut-da-kut da Iran. Sun kasance tare da Iran a lokutan wahala, kuma abu ne mai kyau cewa Iran suna ci gaba da tuntubar juna tare da su a fagage daban-daban, musamman a yanzu da aka tabo batun tattaunawa da Amurka a fakaice.
Araqchi ya ci gaba da cewa: “Suna bukatar su sanar da abokansu da ke kasar China cikakkun bayanai game da abubuwan da ke faruwa tare da tuntubarsu, kuma sun yi hakan a makon da ya gabata a kasar Rasha.” Inda ahalin yanzu suke kasar China, kuma zai isar da sakon shugaba kasar Iran Mas’ud Pezeshkian, kuma idan Allah ya yarda za su yi tattaunawa mai kyau.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: China da Rasha a
এছাড়াও পড়ুন:
Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha
Mai ba da shawara ga Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya bayyana cewa: Hanyar Zangezur wata shiri ne na Amurka don matsawa kasashen Rasha da Iran.
Ali Akbar Velayati mai ba wa Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran shawara kan harkokin kasa da kasa, ya dauki aikin Zangezur (arewa maso yammacin Iran) a matsayin wani aikin Amurka na matsawa kasashen Rasha da Iran lamba.
A cikin wani sako na tunawa da Sheikh Safi al-Din Ardebili, Velayati ya yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi Azarbaijan da mashigar Zangezur, yana mai cewa, “Makiya Iran karkashin jagorancin ‘yan sahayoniyyan duniya da Amurka, suna neman ta hanyar tsare-tsare irin su mashigar Zangezur, don ciyar da manyan ayyukan siyasa a karkashin fakewa da wadannan tsare-tsare.”
Ya kara da cewa, manufar farko ita ce raunana gwagwarmaya da yanke alakar Iran da yankin Caucasus da kuma killace Iran da Rasha ta kasa a kudancin yankin.
Ya bayyana cewa: “Wannan aikin ba wai kawai wani bangare ne na shirin Amurka na maye gurbin Ukraine da yankin Caucasus a matsayin wani sabon fage na matsin lamba kan Rasha da Iran ba, amma ana aiwatar da shi ne tare da goyon bayan kungiyar tsaro ta NATO da kuma wasu kungiyoyin ‘yan kishin kasa na Turkiyya (Pan-Turkist).