Aminiya:
2025-08-02@03:49:26 GMT

Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta 

Published: 1st, August 2025 GMT

Jami’an tsaro sun tabbatar da kuɓutar wasu ɗalibai shida na Makarantar Horon Ilimin Shari’a ta Najeriya da aka sace.

Rundunar ’yan sandan Jihar Binuwai ce ta bayyana hakan a ranar Juma’a.

’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN

Kakakin ’yan sandan, Udeme Edet, ya ce ɗaliban sun taso ne daga Jihar Anambra, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa makarantar horon ilimin shari’a da ke Yola, a Jihar Adamawa.

’Yan bindiga ne suka tare su a iyakar Binuwai da Taraba.

“An ceto ɗalibai shida da aka sace a ranar 26 ga watan Yuli, 2025, yayin da suke kan hanyarsu daga Anambra zuwa Adamawa.

“An sako su lafiya ƙalau kuma sun koma wajen iyalansu a safiyar yau, 1 ga watan Agusta, 2025,” in ji sanarwar.

Maharan sun nemi Naira miliyan 120 a matsayin kuɗin fansa, kuma sun yi barazanar kashe ɗaliban idan ba a biya buƙatarsu ba.

Matsalar na ci gaba da ta’azzara a Jihar Binuwai.

A bara ma, an sace ɗalibai 20 yayin da suke kan hanyar zuwa Jami’ar Jos a Jihar Filato.

Maharan sun sako su bayan shafe makwanni a hannunsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Binuwai Ɗalibai Garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi

Gwamnatin jihar Kano tare da hadin gwiwar wata kungiya mai suna Partnership for Agile Governance and Climate Change (PACE) ta kaddamar da manufofinta na sauyin yanayi a hukumance. Wannan manufa mai mahimmanci ta samar da taswirar dabaru don ragewa, daidaitawa, da tsarin tafiyar da yanayi mai hadewa a duk sassan ci gaba a jihar.

 

Da yake jawabi a wajen taron kaddamar da taron wanda aka gudanar a dakin taro na Armani Event Centre dake Kano, Gwamna Abba Yusuf wanda sakataren gwamnatin jihar Ibrahim Farouk ya wakilta, ya bayyana taron a matsayin wani babban ci gaba a kokarin gwamnatinsa na mayar da jihar Kano a matsayin mai ci gaba a harkokin tafiyar da yanayi da muhalli.

 

Gwamna Yusuf ya jadadda cewa, manufar tana cike da shirin aiwatar da sauyin yanayi, wanda ke fassara kudirin siyasar gwamnati zuwa tsarin aiwatarwa a aikace.

 

 

Ya kuma yi tsokaci kan shirye-shiryen da gwamnati ke yi na samar da makamashi ta hasken rana da ababen more rayuwa.

 

 

Gwamnan ya nanata shirin gwamnatin sa na dasa itatuwa miliyan 5 a shekarar 2025 domin rage zaizaiyar kasa, da inganta iskan shaka, da inganta kyawawan birane.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi