Gwamnan Jihar ta Gwambe, ya tunatar da cewa; a lokacin da Bola Ahmed Tinubu ya tsaya a gabanmu a matsayin ɗan takara a yaƙin zaɓen 2023, ya yi wa Arewacin Nijeriya alƙawura na musamman. Kazalika, Arewa ta amince da manufofin shugaban ƙasar, ta kuma yi tsayin daka wajen zaɓensa, inda suka bayar da gudunmawa na kimanin kashi 60 cikin 100 na ƙuri’un da Tinubun ya samu.

“A yau, ga shi mun taru, domin yin nazari a kan waɗancan alƙawuran tare kuma da tantance irin ci gaban da aka samu ya zuwa yanzu, abubuwan da muka samu su ne; sauye-sauyen da aka samu duk kuwa da irin ƙalubalen da ake fuskanta a wannan ƙasa. Wannan na nuna cewa, demokuraɗiyyarmu za ta iya yin aiki ne kaɗai idan ana cika alƙawuran da aka ɗauka, sannan shugabanni ba za su iya aiwatar da alƙawuran ba har sai sun samu haɗin kan ƴan ƙasa.  

“Zan iya bugun ƙirji wajen bayyana irin ci gaban da yankinmu na Arewa ya samu. ɗon haka, muna yi wa shugaban ƙasa godiya dangane da waɗannan sabbin tsare-tsaren ci gaba da ya kawo mana, mafi yawan ayyukan day a gada daga gwamnatin da ta gabata, yanzu haka yana kan hanyar kammala su.” 

Ya bayyana ire-iren waɗannan ayyuka da suka haɗa da aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano, layin jirgin ƙasa na Kano zuwa Katsina zuwa Maraɗi, gyaran matatar mai ta Kaduna, aikin bututun iskar gas na Abuja, Kaduna, Kano da kuma ci gaba da aikin haƙar mai a Kolmani.

“Waɗannan ayyuka, ko shakka babu; za su kawo ci gaba a ɓangaren masana’antu da samar da tsaro a yankunanmu na Arewa,” in ji shi. 

Gwamna Yahaya ya ƙara da cewa, akwai kuma wasu sabbin ayyukan more rayuwar da ken an tafe, waɗanda suka haɗa da hanyoyi daban-daban a tsakanin jihohi kamar babbar hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, wadda za ta haɗa ƴan kasuwar Arewa da na Kudu da kuma shirin samar da harkokin nomad a zai shafi Arewa.

Bugu da ƙari, ya lissafo wasu da suka haɗa da faɗaɗawa tare da inganta cibiyoyin harkokin kiwon lafiya, wanda y ace; dukkanninsu suna nuni ga manufar da aka tsara, don inganta rayuwar al’ummar wannan yanki na Arewa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna

 

Daga Abdullahi Shettima.

Ƙungiyar taimako mai zaman kanta mai suna Rays Heaven for Special Needs Children and Adults ta gudanar da taron wayar da kai a Kaduna domin ƙarfafa fahimtar muhimmancin kula da lafiyar kwakwalwa da kuma magance matsalolin tattalin arziki da ke shafar rukunin jama’a masu rauni.

Shugaban shirye-shiryen ƙungiyar, Sadiq Abdilatif, ya bayyana cewa wannan shiri mai taken Youth Resilience Project ana aiwatar da shi ne da tallafin Ƙungiyar Tarayyar Turai (European Union) tare da Global Youth Mobilization Fund.

Ya ce manufar shirin ita ce wayar da kai ga makarantun sakandare, al’ummomi, da sansanonin ’yan gudun hijira kan mahimmancin lafiyar kwakwalwa, tare da ƙarfafa matasa su koyi magana idan suna fuskantar damuwa ko matsaloli, da kuma koyar da malamai da shugabannin al’umma hanyoyin taimaka musu.

Mr. Abdilatif ya bayyana cewa matasa da mutane masu buƙata ta musamman, ciki har da ’yan gudun hijira, na fama da ƙalubalen tunani da na tattalin arziki da ke rage musu ƙarfi wajen gudanar da rayuwa. Ya ce wannan shiri yana nufin gina ƙarfin gwiwa da samar da wakilai a cikin al’umma waɗanda za su ci gaba da yada wannan saƙo a yankunansu.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar na da shirin haɗa shugabannin gargajiya da na addini domin tabbatar da ci gaba da wayar da kai a matakin ƙasa, yana mai cewa batun lafiyar kwakwalwa abin ne da ya shafi kowa.

Ɗaya daga cikin mahalarta shirin, Salma Hussaini, wadda ba ta da gani, ta yaba da yadda ƙungiyar ta haɗa masu buƙata ta musamman a cikin shirin. Ta ce ta amfana sosai wajen fahimtar yadda ƙarfin tunani da dogaro da kai ke taimakawa mutum ya shawo kan ƙalubalen da yake fuskanta duk da rashin lafiyar jiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna