Aminiya:
2025-06-15@02:23:39 GMT

NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya?

Published: 21st, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A daidai lokacin da ake tunanin samun sauƙi daga tarin matsalolin tsaro da na tada ƙayar baya a Najeriya, sai ga wasu sabbin matsalolin na ƙara kunno kai.

Yayin da a wannan lokaci ake fuskantar hare-haren da ake zargin na ƙungiyar Boko Haram ne a Arewa maso Gabas, da kuma sabbin kashe-kashe a sassan jihohin Filato da Binuwai, sai kuma ga wata sabuwar ƙungiya da ake zargin ta ’yan ta’adda ce mai suna Mahmuda ta ɓulla a Jihar Kwara.

To ko mene ne ya haddasa wannan koma-baya ta fuskar tsaro?

Shin a ganinku, me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnatin” Najeriya?

NAJERIYA A YAU: Sabbin dabarun hana matasa aikata laifi DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan ƙara ƙazancewar matsalar tsaro da hanyoyin magance su a Najeriya.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Binuwai matsalar tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

  Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki

Majiyar tsaron kasar ta Kamaru sanar da cewa, da dama daga cikin sojojin kasar sun rasa rayukansu sanadiyyar wani hari da kungiyar Bokoharam ta kai musu ta hanyar amfani da manyan bindigogi da kuma jirgin sama maras matuki akan iyaka da Najeriya.

Majiyar ta ce an kai harin ne a yankin Sagami dake kusa da tafkin Chadi a gundumar Logun mai iyaka da kasar Najeriya.

Ita dai kungiyar Bokoharam ta addabi kasashen Najeriya, Kamaru da kuma jamhuriyar Nijar. Yankun arewacin kasar ta Kamaru ya fara fuskantar kai hare-hare daga wannan kungiyar ne tun a 2014 wanda kuma har yanzu yana ci gaba da faruwa daga lokaci zuwa lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
  • NAJERIYA A YAU: June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?