HausaTv:
2025-07-03@03:33:35 GMT

JAN KUNNE: Ɗan Atiku Abubakar ya mayar wa ɗan gwamnan Bauchi zazzafan martani

Published: 16th, April 2025 GMT

Muhammad Atiku wanda ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa ne, ya ce, gwamnna Bauchi, Bala Mohammed, bai taɓa mara wa mahaifinsa baya ba a zaɓukan 2019 da 2023 da aka yi.

Ɗan Atiku na wannan kalamai ne a matsayin martani ga ɗan gwamnan Bauchi, Shamsu Bala wanda ya zargi ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa da yi wa mahaifinsa maƙarƙashiya a zaɓen 2023.

A ranar Asabar ce, Shamsu ya ce Atiku ba ma ya tunanin zuwa ya nemi gafarar mahaifinsa duk kuwa da shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027 da yake yi.

“Bambancin da ake akwai yanzu shi ne Shamsu ya fito fili ya nuna mana cewa ka da mu sa ran samun goyon mahaifinsa (gwamnan Bauchi),” ya faɗa.

Ɗan Atiku Abubakar ya yi wannan martanin ne cikin wani saƙo da ya aiko wa da Premium Times a ranar Litinin, yana mai jaddada cewa gwamnan Bauchi ne ya yi wa mahifinsa zagon ƙasa a zaɓen 2023.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: gwamnan Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Majalisar Dokokin Jihar Filato ta zaɓi Nanloong Daniel a matsayin sabon Kakakin Majalisar, bayan da Gabriel Dewan ya yi murabus.

Zaɓen sabon kakakin ya gudana ne a wani zaman gaggawa da majalisar ta gudanar ranar Laraba.

David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana

Zaman ya gudana ne a harabar tsohon gidan gwamnatin jihar.

Hon. Nanloong Daniel, wanda ke wakiltar mazaɓar Mikang wanda kuma tsohon jagoran masu rinjaye ne a majalisar ta tara, ya samu amincewar dukkanin ’yan majalisar 24 don jagorantar su.

Daniel shi ɗan jam’iyyar APC ne.

Zaɓen nasa ya biyo bayan wani zaman sirri da aka yi tsakanin Gwamna Caleb Mutfwang, tsohon kakakin majalisar Dewan, da sauran ’yan majalisar, domin warware rikicin shugabanci da ke damun majalisar.

Mataimakin akakin ajalisar, Hon. Gwotta Ajang, ne ya jagoranci zaman gaggawar tare da kula da sauyin shugabancin cikin lumana.

Dewan, wanda shi kaɗai ne ɗan jam’iyyar YPP, daga yankin Filato ta Tsakiya, ya ajiye muƙaminsa domin taimakawa wajen kawo ƙarshen rikicin siyasar jihar.

Murabus ɗinsa na zuwa ne bayan wani dogon lokaci aka kwashe ana rikici bayan korar wasu ’yan majalisar jam’iyyar PDP daga majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa