JAN KUNNE: Ɗan Atiku Abubakar ya mayar wa ɗan gwamnan Bauchi zazzafan martani
Published: 16th, April 2025 GMT
Muhammad Atiku wanda ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa ne, ya ce, gwamnna Bauchi, Bala Mohammed, bai taɓa mara wa mahaifinsa baya ba a zaɓukan 2019 da 2023 da aka yi.
Ɗan Atiku na wannan kalamai ne a matsayin martani ga ɗan gwamnan Bauchi, Shamsu Bala wanda ya zargi ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa da yi wa mahaifinsa maƙarƙashiya a zaɓen 2023.
A ranar Asabar ce, Shamsu ya ce Atiku ba ma ya tunanin zuwa ya nemi gafarar mahaifinsa duk kuwa da shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027 da yake yi.
“Bambancin da ake akwai yanzu shi ne Shamsu ya fito fili ya nuna mana cewa ka da mu sa ran samun goyon mahaifinsa (gwamnan Bauchi),” ya faɗa.
Ɗan Atiku Abubakar ya yi wannan martanin ne cikin wani saƙo da ya aiko wa da Premium Times a ranar Litinin, yana mai jaddada cewa gwamnan Bauchi ne ya yi wa mahifinsa zagon ƙasa a zaɓen 2023.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: gwamnan Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
Daga Abdullahi Shettima
Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya karɓi Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda suka tattauna kan manyan muhimman abubuwan ci gaban jihar musamman a fannoni na noma, ababen more rayuwa da tsaro.
A yayin ganawar, Gwamna Uba Sani ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Ƙasa bisa goyon bayan da gwamnatin tarayya ke bai wa Jihar Kaduna, musamman wajen ci gaban harkokin noma da sarrafa amfanin gona. Ya ce kafa Special Agro-Industrial Processing Zone (SAPZ) da African Quality Assurance Centre (AQAC) ya ɗaga martabar jihar a matsayin jagora wajen ci gaban sarkar samar da kayayyakin noma da kuma faɗaɗa damar fitar da su ƙasashen waje. Shugaban Ƙasa ya yaba da wannan cigaba tare da tabbatar da cikakken goyon bayan gwamnatin tarayya.
Haka kuma, Gwamnan ya bayyana wa Shugaban Ƙasa ci gaba da aikin sabunta harkar sufuri a Kaduna, ciki har da aikin Light Rail da kuma tsarin Bus Rapid Transit (BRT) — wanda shi ne na biyu a Najeriya bayan na Legas. Shugaba Tinubu ya tabbatar da ci gaba da tallafi daga gwamnatin tarayya, tare da yabawa da irin hangen nesan Kaduna a bangaren gine-gine.
Shugaban Ƙasar ya kuma tabbatar da aniyar gwamnati wajen ƙarfafa zaman lafiya da tsaro a fadin Jihar Kaduna, tare da alkawarin gaggauta aikin gyara titin Abuja–Kaduna–Zaria–Kano. Ya jaddada cewa gwamnatin tarayya na aiki kafada da kafada da ajandar cigaban Jihar Kaduna domin samar da raya kasa mai fa’ida ga al’umma da inganta rayuwar ’yan ƙasa.
Karshe.