HausaTv:
2025-05-21@21:45:53 GMT

JAN KUNNE: Ɗan Atiku Abubakar ya mayar wa ɗan gwamnan Bauchi zazzafan martani

Published: 16th, April 2025 GMT

Muhammad Atiku wanda ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa ne, ya ce, gwamnna Bauchi, Bala Mohammed, bai taɓa mara wa mahaifinsa baya ba a zaɓukan 2019 da 2023 da aka yi.

Ɗan Atiku na wannan kalamai ne a matsayin martani ga ɗan gwamnan Bauchi, Shamsu Bala wanda ya zargi ɗan tsohon mataimakin shugaban ƙasa da yi wa mahaifinsa maƙarƙashiya a zaɓen 2023.

A ranar Asabar ce, Shamsu ya ce Atiku ba ma ya tunanin zuwa ya nemi gafarar mahaifinsa duk kuwa da shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027 da yake yi.

“Bambancin da ake akwai yanzu shi ne Shamsu ya fito fili ya nuna mana cewa ka da mu sa ran samun goyon mahaifinsa (gwamnan Bauchi),” ya faɗa.

Ɗan Atiku Abubakar ya yi wannan martanin ne cikin wani saƙo da ya aiko wa da Premium Times a ranar Litinin, yana mai jaddada cewa gwamnan Bauchi ne ya yi wa mahifinsa zagon ƙasa a zaɓen 2023.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: gwamnan Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi bankwana da maniyyata 966 da za su je aikin Hajjin bana, inda ya buƙace su da su kiyaye dokoki da tsarin ƙasar Saudiyya.

Gwamnan, ya samu wakilcin Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Abubakar Ibrahim Njodi, wanda ya gargaɗi maniyyatan da cewa duk wanda ya karya doka zai fuskanci hukunci.

Yadda jami’an tsaron Vatican suka hana Seyi zuwa wajen Tinubu da Fafaroma NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?

Gwamnan ya bai wa kowane maniyyaci kyautar Riyal 200 a matsayin goron Sallah.

An kuma ja hankalin maniyyatan da ka da su karɓi kaya ko rigar wani, ko da ’yan jiharsu ne, don kauce wa matsala.

Malaman addini da suka halarci taron sun shawarci maniyyatan da su yi aikin Hajji da nufin samun lada, su nemi ƙarin haske idan ba su fahimci wani abu ba, sannan su yi addu’a don samun zaman lafiya a Najeriya.

Hakazalika, an tunatar da su, su kula da kayansu don kaucewa shiga matsala.

Sakataren hukumar Alhazai na jihar, Alhaji Sa’adu Hassan, ya bayyana cewa aikin Hajji ibada ce, ba yawon shaƙatawa ba, don haka ya buƙace su, da su mayar da hankali wajen gudanar da ibadarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista
  • Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar
  • Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo
  • Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya ba su kyautar Riyal 200
  • Yadda jami’an tsaron Vatican suka hana Seyi zuwa wajen Tinubu da Fafaroma
  • APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa