Harbin dai ya samu Comfort ne a kai, inda nan take ta mutu, yayin da wasu harsasai suka samu mijinta a mukamuki da kafadarsa dama.

Yayin da ‘ya’yansu ke kururuwar firgici, rahotanni sun ce jami’an sun gudu daga wurin.

An kori Musiliu daga aikin ‘yansanda ne a ranar 17 ga watan Satumba, 2015, daga bisani kuma aka bayar da belinsa a shekarar 2017 ba tare da sanin dangin da ya kashewa ‘yan uwa ba.

Bayanan kotun sun nuna cewa mai shari’a O.A. Taiwo na Kotun 26, Babban Kotun Ikeja, ya bayar da belin Musiliu a kan Naira miliyan 1 tare da mutane biyu.

A hukuncin kotun, Mai shari’a Taiwo ya bayyana cewa, “Sashe na 115(1) na dokar shari’a ta shekarar 2011 ya bai wa kotu damar bayar da belin wanda ake tuhuma da laifin kisa.

“Don haka kotu na da hurumin bayar da belin wanda ake tuhuma da laifin kisa ko kuma a’a, hakkin mai nema ne ya nuna ta hanyar bayar da wasu bukatu na musamman wadanda za su bai wa kotu damar yin amfani da damar da ta ga ya dace ga mai bukata.”

Tun lokacin da aka bayar da belin Musiliu, jaridar PUNCH Metro ta gano cewa har yanzu ba a san inda Musiliu yake ba duk da zaman kotun da aka yi da kuma yunkurin kama wadanda za su tsaya masa.

Da yake zantawa da jaridar PUNCH, Godwin Udoh ya bayyana takaicinsa da irin wannan rashin imani.

“Na yi mamaki da ban gan shi (dan sandan) a kotu ba kafin daga baya na gano cewa an bayar da belinsa, babu wanda ya yi tsammanin za a bayar da belinsa.

“Duk lokacin da suka nemi gidan yarin da su gabatar da shi a gaban kotu, sai su ba da uzuri kamar rashin man da za su yi jigilarsa. A haka na fara binciken abin da ke faruwa,” in ji Udoh.

Udoh ya bayyana cewa binciken da ya yi ne ya sa ya gane cewa lallai an saki Musiliu.

“Kotun da ke tafiyar da shari’ar a yanzu tana babbar kotun TBS, amma ba su taba kawo shi wurin domin gurfanar da shi ba, lokacin da aka taba gurfanar da shi a gaban kotun majistare da ke Ebute Metta a shekarar 2015 da lamarin ya faru,” in ji shi.

“Alkalin mai shari’a, Hon. Justice Akintoye, har ma ya rubuta wa dukkan gidajen yarin Jihar Legas wasiku, amma sun ki gabatar da wannan mutum a kotu, har ma sun bayar da sammacin kama mutum biyun da za su tsaya masa.

Udoh ya koka da cewa, “Kotun gaba daya ba ta yarda an bayar da belinsa ba, sai da ni kaina na je na gano shi, a lokacin ne na tabbatar da cewa kotun Honarabul Taiwo da ke Ikeja ta bayar da belinsa, yanzu mutumin ya bace, ba mu sake jin komai a kansa ba.”

Har yanzu dai ana ci gaba da shari’ar, inda aka shirya zaman kotu na gaba a ranar 9 ga watan Afrilu, sai dai Udoh bai da tabbas ko za a yi adalci.

“Babu wanda ya tsaya masa a kotu a matsayin lauyansa, sai dai mai gabatar da kara daga ma’aikatar shari’a ta Jihar Legas ya ce in yi kokarin ganin su a Alausa domin su samu hanyar gurfanar da shi a gaban kotu,” in ji shi.

Udoh, yayin da yake tunani a kan rayuwarsa bayan wani mummunan lamari da ya faru a shekarar 2015, ya bayyana cewa an bar shi da ‘ya’yansa suna kokawa su kadai, duk da alkawuran da shugabannin ‘yansanda suka dauka na tallafa musu.

“Ciwon da nake ji daga wannan rauni har yanzu ba na iya jurewa,” in ji shi.

“Har yanzu akwai wani karfe a cikin mukamukina da ya kamata a cire, likitan ya ce suna bukatar fitar da shi a maye gurbinsa da kashi don in iya tauna da kyau. Amma yayin da nake magana da ku, karfen yana ci gaba da cutar da ni.

Udoh ya kuma tunatar da yadda ‘yansanda suka kasa taimakawa wajen binne matarsa marigayiya a shekarar 2016.

“Na gana da kwamishinan ‘yansandan Jihar Legas, amma ya ce min ‘yansanda ba sa binne kowa kuma in yi da kaina,” in ji shi.

Ya koka da cewa duk da tabbacin da ‘yansandan suka yi sun yi watsi da shi da iyalansa.

“Sun yi alkawari za su kula da ni, da biyan duk kudin da nake kashewa na jinya, da kuma tabbatar da cewa an yi mini tiyatar da ta dace, amma sun bar ni ina shan wahala.

“Kudin aikin cire wannan karfe daga mukamukina ya kai miliyoyin Naira, kuma ba ni da wannan kudin,” in ji shi.

Udoh ya ci gaba da bayyana cewa, rundunar ‘yansandan ta kuma yi alkawarin tallafa wa ‘ya’yansa na kudi, kula da lafiya, da bayar da tallafin karatu.

“Sun ce za su saka ni a cikin lissafin albashi don in sami akalla tallafin kudi a kowace shekara. Babu wani abu da ya faru,” in ji shi.

Hatta takardar shedar karatu da aka bai wa ‘ya’yansa daga baya an dawo da su.

“Sun ce kuskure ne kuma za su gyara su mayar da shi ga sufeto-janar domin ya amince min, har yau ban samu ba.”

Ta’asar da ‘yansanda ke yi wa fararen hular da ba su ji ba ba su gani ba ya zama ruwan dare duk da kokarin da ake na shawo kan jami’an da ke da ra’ayin aikata laifuka.

Rundunar ‘yansandan ta kori Sufeto Usman Dikko daga mukaminsa bisa rasuwar Baale na Lotu, Marigayi Cif Fatai Jubril, a shekarar 2023.

An kori wani jami’in da ya yi wa wata yarinya fyade da bindiga a cikin ofishin ‘yansanda a Legas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Naira bayar da belinsa bayar da belin bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran

Iran ta sanar da soke zaman tattaunawa da ya kamata ta yi da Amurka kan batun nikiliyarta a Oman yau Lahadi saka makon hare-haren da Isra’ila ta kai mata a ranar Juma’a.

Bayanai sun ce a wannan Lahadin ce ya kamata a gudanar da ganawa ta shida tsakanin wakilan Amurka da na Iran a birnin Musqat na Oman.

Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

Sai dai kakakin Ministan harkokin wajen Iran, Esmaeil Baqaei ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, Amurka ta nuna fuska biyu, inda a gefe guda take tattaunawar cimma masalahar jingine ƙera nukiliya da Iran, amma a ɗaya gefen kuma ta goyi bayan harin da Isra’ila ta kai mata.

Iran ta zargi Amurka da goyon bayan harin da Isra’ila ta kai mata, sannan kuma ta ce tattaunawar yarjejeniyar dakatar da ƙera makamin ƙare dangi na nukiliya da take yi da Amurkar ba ta da wani amfani.

A nasa ɓangaren, Ministan harakokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce babu buƙatar ci gaba da tattaunawa da aka faro tsakiyar watan Afirilun wannan shekara lura da harin dabbanci da Isra’ila ta kai mata.

Kafofin yaɗa labarai da dama a Iran sun shaida cewa guda daga cikin masu baiwa jagoran addinin musluncin Iran ayatoAllah Ali Khamenei kuma mai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar, Ali Shamkhani, na daga cikin waɗanda su ka ji rauni a hare-haren na Isra’ila.

Tun farko Isra’ila ce ta fara kai wa Iran hari kan cibiyoyin nukiliyarta tare da halaka manyan hafsoshin tsaronta, cikin daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a, kuma ta ci gaba da kai farmaki da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, mafarin buɗe kofar wani sabon rikici a tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna adawa da juna tsawon shekaru.

Harin ramuwar gayya da Iran ta kai wa Isra’ila da safiyar Asabar ya halaka mutane uku, tare da jikkata wasu da dama a biranen Jerusalem da Tel Aviv, inda hukumomin Isra’ila ke ci gaba da gargaɗin ‘yan kasar su nemi mafaka.

A wani jawabi da jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gabatarwa al’ummar kasar ranar Juma’a, ya ce ba za su saurara wa Isra’ila ba sakamakon munin abin da ta aikata musu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2