Leadership News Hausa:
2025-07-31@00:46:08 GMT

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

Published: 4th, April 2025 GMT

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, ya ce: “Ko muna so ko ba mu so, lokaci ya yi da za mu yi bankwana.”

Ƙungiyar Manchester City ta ce za ta shirya wani bikin bankwana na musamman domin girmama ɗan wasan kafin kakar ta ƙare.

De Bruyne ya koma City daga Wolfsburg a kan fan miliyan 55, kuma ya taimaka sosai wajen nasarorin da ƙungiyar ta samu, ciki har da lashe kofin Zakarun Turai karo na farko a tarihinta, inda suka doke Inter Milan a wasan ƙarshe a birnin Istanbul.

Sai dai ɗan wasan ya sha fama da rauni a ‘yan shekarun nan, inda ya shafe watanni biyar yana jinya a kakar da ta wuce.

A kakar bana, ya buga wasanni 26 kacal a dukkanin gasa.

De Bruyne, ya fara wasan ƙwallon kafa a kulob din Genk na Belgium, kafin Chelsea ta saye shi a watan Janairu 2012 a kan fan miliyan bakwai.

Ya buga wa Chelsea wasanni tara kacal sannan aka tura shi aro zuwa Werder Bremen, daga nan ya koma Wolfsburg a 2013, kafin komawarsa City.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barin Kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai

Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.

A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.

Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane Da Dama A Yola
  • Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo