Leadership News Hausa:
2025-04-30@23:26:15 GMT

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

Published: 4th, April 2025 GMT

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, ya ce: “Ko muna so ko ba mu so, lokaci ya yi da za mu yi bankwana.”

Ƙungiyar Manchester City ta ce za ta shirya wani bikin bankwana na musamman domin girmama ɗan wasan kafin kakar ta ƙare.

De Bruyne ya koma City daga Wolfsburg a kan fan miliyan 55, kuma ya taimaka sosai wajen nasarorin da ƙungiyar ta samu, ciki har da lashe kofin Zakarun Turai karo na farko a tarihinta, inda suka doke Inter Milan a wasan ƙarshe a birnin Istanbul.

Sai dai ɗan wasan ya sha fama da rauni a ‘yan shekarun nan, inda ya shafe watanni biyar yana jinya a kakar da ta wuce.

A kakar bana, ya buga wasanni 26 kacal a dukkanin gasa.

De Bruyne, ya fara wasan ƙwallon kafa a kulob din Genk na Belgium, kafin Chelsea ta saye shi a watan Janairu 2012 a kan fan miliyan bakwai.

Ya buga wa Chelsea wasanni tara kacal sannan aka tura shi aro zuwa Werder Bremen, daga nan ya koma Wolfsburg a 2013, kafin komawarsa City.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barin Kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

CP Bakori ya gode wa al’ummar Kano saboda goyon bayan da suke ba su a ƙoƙarin su na yaƙar masu aikata laifuka tare da kira ga ci gaba da haɗin kai wajen kai rahoton abubuwan da suke zargi ga Ƴansanda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano