Ya kara nuna shakku kan dalilin da ya sa aka kafa dokar ta-baci a Jihar Ribas, yana mai cewa rashin tsaro ya addabi wasu sassan kasar nan, amma ba a kakaba dokar ta-baci ba ko kuma wani abu makamancin haka.

“Idan shugaban kasa ya ce saboda rashin tsaro ne, saboda sun fasa bututun mai, yaya batun sassan kasar da ake fama da rashin tsaro? Shugaban kasar yana cewa su ma su kafa masa dokar ta-baci a kansa.

Ba za su iya ba, saboda shi shugaban kasa ne da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya, babu wanda zai iya sanya masa dokar ta-baci, saboda akwai rashin tsaro mai tsanani a arewa maso gabas, arewa maso yamma, hatta a kudu maso gabas da kudu maso yamma, amma ba a saka dokar ta-baci ba sai a Jihar Ribas.”

Amaechi ya jaddada cewa alhakin tsaro ya rataya ne a wuyan gwamnatin tarayya, ba gwamnonin jihohi ba, wanda hakan ya sa dakatarwar Fubara ba ta dace ba.

“Gwamnan Ribas ba shi da alhakin tsaro, ya rataya a wuyan shugaban kasa, to me zai sa a hukunta mutumin da bai aikata wani laifi ba?” Ya tambaya.

Tsohon gwamnan na Ribas ya zargi Tinubu da saba ka’idojin tsarin mulki na yadda za a cire gwamna daga mukaminsa.

“Shugaban ya yanke hukunci ne ta wajen kundin tsarin mulki. Sashe na 188 ya bayyana yadda gwamna zai bar mulki, ko dai ya mutu, ko murabus, ko kuma a tsige shi. Amma bai ce wata rana ka farka ba, wani mutum da ake kira shugaban Nijeriya zai fid da ka daga mulki, wanda hakan ya saba wa dimokuradiyyar Nijeriya.”

Amaechi ya yi kira ga mazauna Ribas da su bijire wa dokar ta-baci, sannan ya bukace su da su yi zanga-zangar lumana wanda dimokuradiyya ta amince da shi.

Da yake magana kan rikicin siyasar da ke faruwa tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Gwamna Fubara, Amaechi ya yi zargin cewa rikicin kudi ne kawai.

“Abun da ke faruwa a tsakanin Gwamnan Jihar Ribas na yanzu da Ministan Babban Birnin Tarayya, shi ne batun raba kudi, idan ba haka ba, mene ne na rigima? ‘Yan Nijeriya ba sa son cin hanci da rashawa a wannan lokaci, ban ga wani a kan titi yana tambayar ko mene ne matsalar ba, ko su biyun za su iya magana da jama’a su fada mana matsalar?”

Amaechi ya koka da yadda a yanzu Jihar Ribas na karkashin mulkin soja ne, inda ta hana ‘yan kasar cin ribar dimokuradiyya.

“Yanzu an hana mu cin gajiyar dimokuradiyya. Jihar Ribas ce kadai jihar da ba ta jin dadin dimokuradiyya a halin yanzu, sun kakaba mana mulkin soja da karfin tsiya,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dokar ta baci rashin tsaro Jihar Ribas

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8

Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

A cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.

Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.

“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.

Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe