Amurka : Trump Ya Katse Tallafin Jami’ar Columbia, Saboda Zanga-zangar Goyon Bayan Falasdinu
Published: 9th, March 2025 GMT
Shugaban Amurka Donald Trump, ya katse tallafin da yake baiwa jami’ar Columbia saboda zanga-zangar goyan bayan Falasdinu.
Trump ya ce an katse tallafin na dala miliyan 400 ga jami’ar, daya daga cikin manyan a kasar, bisa zarginta da gazawa wajen fuskantar ayyukan kyamar Yahudawa a harabarta, wanda ke nufin zanga-zangar goyon bayan Falasdinu.
Ana kallon wannan a matsayin alwashin da Donald Trump, ya sha a lokacin yakin neman zabe inda sha yin tir da yadda wasu jami’o’i ke nuna gazawa wajen fuskantar zanga zangar goyan bayan Falasdinu.
Masana da dama na ganin matakin a matsayin misali na siyasantar da manyan makarantu da kuma tsoma bakin gwamnati.
Shugaban kungiyar jami’o’in Amurka ya bayyana cewa matakin na gwamnatin Trump “ya haifar da matukar damuwa game da sha’anin ilimi da kundin tsarin mulkin Amurka kan ‘yancin fadin albarkacin baki.
Dama Trump ya sake nanata barazanarsa a wannan makon, inda ya yi alkawarin rage kudaden da ake ba duk jami’ar da ta ba da damar gudanar da zanga-zanga ba bisa ka’ida ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
Dakarun kare juyin musulunci na Iran sun fitar da bayani a lokacin tunawa da sace jami;an diplomasiyyar Iran 4 a birnin Beirut, wanda ya kunshi cewa: Ya zama wajibi ‘yan sahayoniya su kwana da sanin cewa; Duk laifukan da su ka aikata a baya za a yi musu sakamako a kansa,kuma duk wani sabon wuce gona da iri, zai gaggauta zuwa karshensu ne.”
Sanarwar ta kuma ce: Muna tunawa ne da zagayowar cikar shekaru 42 daga wancan aikin ta’addanci, da a yanzu kwanaki kadan ne su ka wuce na kawo karshen yakin da HKI da Amurka su ka kallafa mana na tsawon kwanaki 12. Yaki ne wanda martani mai karfi da jamhuriyar musulunci ta Iran ta mayar yake kara fito da raunin da wannan kirkirarriyar kasa take da shi.
Har ila yau bayanin na dakarun kare juyin musulunci na Iran ya bayyana yadda jamhuriyar musulunci ta Iran ta yi ta kokari a fagen diplomasiyya akan batun jami’an diplomasiyyar da Isra’ila ce ta sace su ta hanyar ‘yan korenta,kuma hatta babban magatakardar MDD a 2008 ya bayyana cewa a shirye yake ya bayar da hadin kai domin ganin an warware batun,amma kuma abin takaici har zuwa yanzu wadanda su ka aikata laifin ba su fuskanci sakamakon da ya dace da su ba.
A dalilin haka dakarun kare juyin musuluncin suke kara tunatar da MDD da kuma kungiyar agaji da “Red Cross” da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu akan wannan batun. jami’an diplomasiyyar da HKI ta yi garkuwa da su sun hada janar Alhaj Ahmad Mutawassiliyan, sai Sayyid Muhsin Musawi, Taki Rastigar Mukaddam, da kuma Kazim Akawan.