Shugaban Amurka Donald Trump, ya katse tallafin da yake baiwa jami’ar Columbia saboda zanga-zangar goyan bayan Falasdinu.

Trump ya ce an katse tallafin na dala miliyan 400 ga jami’ar, daya daga cikin manyan a kasar, bisa zarginta da gazawa wajen fuskantar ayyukan kyamar Yahudawa a harabarta, wanda ke nufin zanga-zangar goyon bayan Falasdinu.

Ana kallon wannan a matsayin alwashin da Donald Trump, ya sha a lokacin yakin neman zabe inda sha yin tir da yadda wasu jami’o’i ke nuna gazawa wajen fuskantar zanga zangar goyan bayan Falasdinu.

Masana da dama na ganin matakin a matsayin misali na siyasantar da manyan makarantu da kuma tsoma bakin gwamnati.

Shugaban kungiyar jami’o’in Amurka ya bayyana cewa matakin na gwamnatin Trump “ya haifar da matukar damuwa game da sha’anin ilimi da kundin tsarin mulkin Amurka kan ‘yancin fadin albarkacin baki.

Dama Trump ya sake nanata barazanarsa a wannan makon, inda ya yi alkawarin rage kudaden da ake ba duk jami’ar da ta ba da damar gudanar da zanga-zanga ba bisa ka’ida ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar Ansaru

Wata Kotun Tarayya da ke Abuja, ta sanya ranar 15 ga watan Janairun 2026, don fara shari’ar shugabannin ƙungiyar ’yan ta’adda ta Ansaru; Mahmud Usman da Abubakar Abba.

Ana zargin su da jagorantar ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, kuma Hukumar DSS ce ta kama su tare da gurfanar da su a kotu.

Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi Hakimi ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana

An tsara faea sauraren shari’ar a ranar Laraba, amma aka ɗage bayan lauyoyin waɗanda ake tuhuma sun nemi a ƙara musu lokaci.

Lauyansu, B.I. Bakum, ya bayyana cewa har yanzu suna jiran takardun zargi da wajen DSS.

Haka kuma, ya nemi a mayar da waɗanda ake tuhuma zuwa gidan gyaran hali domin suke samun damar ganawa da lauyoyinsu cikin sauƙi.

Lauyan DSS, David Kaswe, ya ƙi aminta da wannan buƙata.

Ya ce lauyoyin dole ne su rubuta wa DSS buƙatunsu kafin su ziyarci waɗanda ake tuhuma.

Alƙalin kotu, Emeka Nwite, ya yanke shawarar bai wa lauyoyin waɗanda ake tuhuma ƙarin lokaci domin shirya wa shari’ar.

Ya ce wannan zai tabbatar da adalci, sannan ya sanya ranar shari’a 15 ga watan Janairun 2026, domin fara sauraren shari’ar.

DSS, tana zargi waɗanda ake tuhuma da jagorantar kai harin gidan yarin Kuje da ke Abuja a 2022, inda fursunoni sama da 600 suka tsere.

Hakazalika, ta zarge su da kai hari wajen haƙar ‘uranium’ a Jihar Neja, tare da sace mutane da dama, ciki har da injiniyan ƙasar Faransa, Francis Collomp, a shekarar 2013.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar
  • Daliban Jami’ar st Gorges Ta Birnin London Sun yi Zanga-zangar Nuna Adawa Da Daukar Tsohon Sojan Isra’ila Aiki
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
  • Iyalan Waɗanda Aka Kashe Yayin Zanga-zangar Bangladesh Sun Yi Maraba Da hukuncin Kisan Tsohuwar Firaminstar
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Iran Ta yi Gargadi Game Da Sakamakon Da  Zai Iya Faruwa A Yankin Bayan Shigar Isra’ila Kasar Siriya
  • Hamas Tayi Gargadi Game Da Kara Dagulewar Al’amura Bayan Harin Isra’ila A Gaza
  • Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar Ansaru